Barka da zuwa shashin musulunci manufar bude wannan shafin shine Bayyana Yadda Musulunci Ya Haskaka Rayuwarmu

kallon film ga ma,aurata

kallon film ga ma,aurata

 Kallon Blue film ga ma'aurata DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA Slm Malam dan.ALLAH yahalatta mutumin da yake da aure yaringa kallon BLUE FILM shida matarsa ? AMSA ========================== ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ . A'a bai halattaba, yin hakan haramunne, Allah (s.w.t) ya tsinewa mai kallon tsiraici da wanda yake nunuwa. Akwai zunubi mai tarin girma, domin gudun kada mutum yafada zina yasa yayi aure, idan akace mutum yayi aure baya samun biyan bukata da matarsa ta sunnah dole saiya kalli kafirai maqiya Allah da Manzonsa suna tafka masha'a suna aikata zuna a fili yazama auren nasa bai katangeshi daga zina ba kenan. Duk ma'auratan da suka sabarwa kansu da irin wannan muguwar dabi'ar tunda wuri sudaina. Bazasu ta6a samun biyan bukata ta wannan hanyar ba. ABIN DAYA KAMATA SUYI SHINE: ================= matsayinsu na ma'aurata su cire kunya su zauna su tattauna tsakaninsu, akan shi mai gidan ko ita uwar gidan wanne abu yafiso ko wanne abu tafiso tayi masa ko yayi mata a lokacin kwanciyarsu ta aure ??? Wannan shine matakin daza su dauka amma maganar kallon B.f haramunne Allah (s.w.t) yana fushi da ma'auratan da basa kishin junansu. Da fatan ma'aurata zasu kiyaye. Allah ka aurar da matasanmu maza da mata su huta da wannan bala'in albarkacin Muhammadu Rasulullah (s.a.w). Dan Allah kudinga yin share dinsa ta facebook da kuma whatsapp domin 'yan uwanku su amfana. www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 9

darasi na 9

Darasi na 9 DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA ***{Darasi na 9}*** Hukunce Hukuncen Azumi. Malam yace: ........... ﻭﺍﻟﺼﻴﺎ ﻡ .......... Ma'ana: Da (sanin hukunce hukuncen) Azumi. BAYANI: Wajibine akan duk wani mukallaf mai hankali yasan hukuncin Azumi, wadannan kuwa sune: 1- Sharudan Azumi. 2- Rukunan Azumi. 3- Abubuwan da suke vata Azumi. 4- Abubuwan da aka karhantawa mai Azumi. 5- Sunnonin Azumi. Duk wadan nan ya kamata mai azumi yasansu. kuma Insha Allah zamuyi bayaninsu daya bayan daya. Musani Azumi yana daga cikin manya-manyan ayyukan da ake bautawa Allah (S.W.T). Saboda girmansa nema Ubangiji madaukakin sarki yake cewa: Azumi nawa ne acikin hadisin da Bukhari da Muslim suka ruwaito cewa: "DUK WANI AIKIN DA DAN ADAM YA AIKATA WANNAN NASANE SAI DAI AZUMI SHI WANNAN NAWANE, NINE KUMA NAKE YIN SAKAYYA IDAN ANYISHI". Saboda girmansa da Albarkar dake cikinsa ne yasa Sahabbai idan yakusa qarewa suke kuka kuma suke fatan Allah ya nuna musu wani. Allah yanuna mana wannan wata lafiya yabamu ikon azumtarsa. Yasa muna cikin wadanda za'a 'yanta a cikinsa. Darasi nagaba zanci gaba. INSHA ALLAH. www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM,WHATSAPP, da sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.Manzon Allah (saww) yace:"WALLAHI IDAN ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA DALILINKA,YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAKUMMA"
Share:

tambaya


MENENE HUKUNCIN MACEN DA TAYI AURE KAFIN TAYI ISTIBRA'I ??? DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA Salam Malam Ya kamata ace nayi istibra’i kafin nayi aure, amma banyiba, har nayi aure, yanzu haka ina jini na farko banyi tsarki ba, amma bada wanda na aikata laifin cikin nayi aure ba. Yaya ingancin aure na? Gani nake kamar babu auren ko ? (Dan Allah ka6oye sunana) AMSA ========================== ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ . DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI. Da farko dai inayi miki wasici da tsoron Allah, saboda zunubin da kika aikata na zina, amma gameda aure, shi aurenki yayi, saidai yinsa bayan istibra’i shine yafi alkhairy, sannan ya wajaba mutukar kinsan kinada ciki to bai halatta kibawa sabon mijinki dama ya take kiba ma'ana ya sadu dake. Saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare Shi: “Duk wanda yayi imani da Allah da ranar lahira, to kada ya shayar da ruwansa ga shukar waninsa”. (Abu-Dawud: hadisi mai lamba 1847). Don haka, ya wajabta a gareki kiyi stibra’i kafin mijinki yasadu dake, sannan istibra’i jini dayane, idan kuma har kin dauki ciki, kafin kiyi istibra’i, in kin haihu kafin wata shida to ba ‘dansa bane, amma in har kin haihu bayan wata shida (6) daga fara saduwarku, to ‘dansa ne, mutukar ba’a samu shaidar da take nuna kinada ciki ba, tun kafinku fara saduwar. WALLAHU A'ALAM DoMIn neman Karin bayani kuduba: (Al-mugny na Ibnu Qudaamah, mujallady na 8\79). www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ Domin samun shafinmu a whatsapp seku dannah wannan, https://chat.whatsapp.com/2AKME7ArAoc5mbmV0dDkWe وسلم عليكم ورحمت وبركاته
Share:

hakkin wanda yaki amsa sallama

hakkin wanda yaki amsa sallama

Hukuncin wanda yaki amsa sallama. DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA Menene hukuncin wanda akayi masa sallama amma yaqi amsawa, kodai saboda girman kai ko kuma saboda wani dalili ??? (Daga Hafiz Ibrahim). AMSA: ===================== ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ . DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI. kada kadamu kaida kayi masa sallamar bakayi asara ba. Aduk lokacin da kayiwa mutum sallama, idan ya amsa kana da lada yana da lada, idan kuwa yaqi amsawa wadanda suka fishi daraja da mutunci (mala'ikun rahama) sun amsa maka. Akwai wanda za'a yiwa gaisuwa 'Assalamu Alaikum'. Yaqi amsawa, saboda shi (yana ganin) ba dama ne, yana jijji da kansa, ko kuma wanda za'a gaishe shi saboda wani banbanci na aqida, shi bai yarda da imanin kaba. Don haka sai yaqi amsawa. Kaga wannan kuwa jahilci ne yake kawo haka. Wannan ba dabi'a bace ta "Ahlus Sunnah". Don haka idan kayi masa sallama ya amsa kai dashi kunyi tarayya cikin lada, in yaqi amsawa kuwa to, wannan shine yayi asara, kai kam bakayi asara ba. Sannan mala'ikun rahma sun amsa maka, Kamar yadda hadisai da sunnah suka koyar. WALLAHU A'ALAM. Allah yabamu ikon gyarawa. www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

tambaya

tambaya

Malam wai da gaskene kowane musulmi sai yashiga wuta ?

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

                      tambaya

Malam wai da gaskene cewar, kowa sai ya dandana wutar lahira, banda Annabi Muhammad (S.A.W.) ?

(Daga Dahiru Adam).

AMSA:
*******************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI. A’a cewa akayi “WADDUHA” ba cewa akayi “MUTHEEQUHA”ba.
Watau kowa sai yabi takan wuta sannan ya wuce. Domin Siradi, akan wuta aka dorashi, mutanen da aka yiwa hisabi zuwa Aljanna sai sunbi takan Siradin. Wanda yake a kan wuta. Shine (acikin Alkur’ani) akace: “WA-IN-MINKUM-ILLA-WARIDUHA KAN-
ALARABBUKA HATMAN MANKIYYA.
Suratul Maryam. Amma kuma jin zafinta (wutar) sai wanda Allah ya nufa da yaji zafin nata, sannan yaji zafin.
Allah ka tseratar damu daga azabar wuta.
WALLAHU A'ALAM.

www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Darasi na 8


Darasi na 8

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA


*****{Darasi na 8}*****

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

MUHIMMANCIN TSARKI.

MALAM YACE:
... ﻭﺍﻟﻄﻬﺎﺭﺓ ...
WAD-DAHARATU
Ma'ana: Da (hukunce hukuncen) tsarki".
BAYANI: Yazama wajibi wato dolene duk wani baligi mai hankali yasan hukuncin tsarki gaba daya, domin tsarki dashi akeyin.

♣Sallah.
♣Azumi
♣Dawafi da sauransu.

Allah madaukakin sarki yana cewa a suratu Baqra ayata 221 wato:
ﺇﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻳﺤﺐ ﺍﻟﺘﻮﺍﺑﻴﻦ ﻭﻳﺤﺐ ﺍﻟﻤﺘﻄﻬﺮﻳﻦ
Ma'ana:
"HAQIQA ALLAH YANA SON MASU YAWAN TUBA,SANNANYANA SON MASU YAWAN TSARKI"
Manzon Allah (S.A.W) yana cewa: "Allah bazai karvi sallar da ba'ayi tsarkiba. Awani hadisin kuma yace:
Babu sallah ga wanda bashi da Alwala.
Awani hadisin kuma yace: Wanda yayi sallah batare da Alwalaba, kuma ya gasgata hakan to shi kafirine. Kunga sallah bata yiwuwa saida tsarki abin tsoratarwar kuma shine: Manzon Allah (S.A.W) yace:
"Banbancin Musulmi da kafiri sallah" Wani hadisin kuma yace:
"Sallah itace ginshiqin Addini, wanda ya tsayar da ita, to ya tsayar da addininsa.
Wanda kuma yabarta to yabar addininsa.
Wani hadisin yace:
Farkon abinda za'a fara tambayar mutum bayan mutuwa shine sallah. Idan ta gyaru komai ya gyaru. Idan kuma ta 6aci komai ya 6aci.Gashi ita kuma Sallar ba'a karvarta saida tsarki. Ya Allah ka tsarkakemu da imaninmu. Sai gobe kuma idan Allah yakaimu lokaci kamar
wannan zamuci gaba.
Insha Allah.

www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

tarkon shaydan akan dan adam

tarkon shaydan akan dan adam

👹Tarkon Shaydan akan dan adam👹 DAGA ZAUREN 🕋HANYAN***TSIRA🕋 TARKUNAN SHAIDAN GUDA 6 AKAN DAN ADAM. Tarkon farko na shaiɗan shine: Yasa a kafircewa Allah ta hanyar * shirka, domin yasan idan aka mutu a haka baza'a samu rahamar ubangiji ba. Idan ka tsallake wannan sai yakaika mataki na biyu. *karamar shirka. Domin yasan tana ruguza kyawawan ayyuka. Idan ka tsallake wannan saiya kaika mataki na gaba. *Zalunci. Yasaka kadinga zaluntar jama'a domin yasan koda kana ayyukan alheri abanza, domin dasu zaka biya bashi. Mata ki nagaba *ya ruguza maka tsarin rayuwa, kazama bakasan muhammancin lokacin kaba, kana ɓata lokutanka agurin abubuwan da aka haramta maka. Mataki nagaba, *rage kaifin ayyukan alkhairi, yasa kadinga qinyin mai muhimmanci kana barin mafi muhimmanci. Sai takun karshe * yasanya ƙiyayya da zolaya awajan mutanan da yayi nasara akansu. Ya zamto kullun in banda isgili da tsokana ba abinda yakeyi da zuciyar wadanda yayi nasara akansu, har zuwa ranar mutuwa harka sauka daga kan gaskiya. Ya Allah ka tsaremu daga sharin shaytan la'ananne. Dan Allah kuyi share ta facebook/whatsapp saboda 'yan uwanku su amfana. www.hanyantsira.blogspot.com 📗📘 whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sai kuyi searching "hanyan tsirah* Koh kudanna nan kuyi like 👇 👇 https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

labarin wani sarki

labarin wani sarki

LABARIN WANI SARKI MAI HIKMA. DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA Dan uwa/ yaruwa bani minti biyu ka daure ka karanta zuwa karshe: tare dayin share wa yanuwa:;.... LABARIN WANI SARKI MAI HIKIMA. Acan wajajen kasashen gabas akai wani Sarki daya dade akan gadon sarauta yana mulki, daya fuskanci ya tsufa sai ya yanke shawarar yin murabus, to amma inda Gizo ke sakar shine wanda zai gajeshi, maimakon kawai ya zabi wani daga cikin yayansa ko a mukarrabansa (yan majalisarsa) sai yasa aka tara dukkan samarin garin a fadarsa, yace musu, " Shekaru sun cin mini, lokaci yayi a gareni da zan koma gefe in nada Magaji, kuma a cikinku na yanke shawarar zaba" Matasan nan duk suka rude wannan ya kalli wannan, wancan yadubi wancan, zuciyarsu cike da tunanin ta yaya ? sarkin yaci gaba da cewa: Yanzu zan baku iri na shuka (seed) kowa yaje ya shukashi, yabashi ruwa ya kula dashi har tsawon shekara guda, akawo min naga irin abin da zaku samu, duk wanda na zabi tasa shine sabon sarki a wannan masarauta. Aka raba wa matasa iri daban-daban kowa yatafi gida cike da burin zama sarki idan shuka tayi kyau. Cikin matasan nan da aka ba akwai wani da ake kira Bilal, da zuwansa gida sai ya shaidawa Mahaifiyarsa dukkan yadda ta wakana a fadar Sarki, tayi murna dajin wannan labari, nan take ta taimaka masa da tukunya da kasa mai kyau wadda zatayi saurin shuka, suka shuka irin nan na sarki. Kowace rana Bilal yakan ba shuka ruwa, sai yayi tsaye yana kallo yaga yadda zata fito,haka yayi tayi har wajen sati uku, amma abin mamaki ba abin daya fito daga kasa, yazuba ido har zuwa na hudu na biyar kai har na zuwa shida amma ko tsagewa kasar batayi ba, ballatana shuka ta fito. Zance ba haka yake ba acikin gari, domin matasa sai murna suke shukarsu sai girma take tanayin kyau, hakan ba karamin tayar da hankalinsa yayiba, sannan gashi duk inda yaje maganar kenan, sai yayi shiru kurum, bai sanar da kowa abin dake faruwaba. A kwana a tashi har wata shida suka shude, matasa a gari nacike da farin ciki, shi kuwa Bilal na cikin damuwa, yanata zuba ruwa ba shuka, kullum zuluminsa yazai fuskanci sarki da tukunya ba komai. Ina ya Allah,babu ya Allah, shekara kwana,inji yan magana, ranar da Sarki ya alkawarta tacika, gari ya zama tamkar ranar Sallah, ko'ina matasa zaka gani dauke da tukunyar bishiya iri daban-daban sunyi kyau ga tsayi, sun wa fadar Sarki tsinke. Amma al'amarin Bilal kuwa awannan rana yatashi ne cikin fargaba har saida Mahaifiyarsa ta kwantar masa da hankali ta ce "kaje da abin da kasamu ya fi kin zuwa kanada gaskiya, kuma kokarin kake nan" Da shigarsa, sai fada ta kaure da dariya da sowa, ana nuna shi da tukunyarsa ba komai, yasami gefe daga baya can kurya ya rakabe tareda sunkuyar da kai kasa, gabansa na dakan uku-uku. Can jimawa sai Sarki ya suitors fada, kowa yaduka yakai gaisuwa sannan akai shiru ana sauraransa, zuciyoyi cike da fata da burin dacewa a samu sarauta, haka abin yake ga jama'ar gari wadanda sukai dako ko Allah zaisa nasu yafito cikin nasara. Sarki yayi murmushi gami da tashi yana tafiya cikin kasaita da ganin shuke-shuke iri daban- daban. "Yace yau itace ranar dana alkawarta muku cewa daya daga cikinku zai zama sabon Sarki a masarautar nan kuma na yaba da abin da idanuna suke ganemin, a saboda da haka...katsam! saiya hango tukunya ba komai aciki mutum a gefe na boyewa, nan da nan yayi umarni da azo da ita damai ita. Bilal yaji wata rashin lafiya gaba daya ta kamashi, cikinsa sai kululu yakeyi, yaji kafafuwansa sun kasa daukarsa "shikenan na kashe irina za a kasheni" yafada a zuciyarsa. Bai gama tunanin yaji anyi sama dashi sai gaban Sarki, ai tuni sai fada ta rude da dariya da kyakyaci da sowa, wasu harda faduwa dan mugunta. Sarki ya daga hannu nan take kowa yayi shiru, waje yayi tsit. "ya sunanka?" Sarki ya tambaya. "Suna na Bilal" yafada jiki na rawa. Sarki ya dubeshi sannan ya dubi taron jama'a cikin murya mai karfin sauti da izza ya ce "Kuyi gaisuwa ga sabon Sarkinku mai suna Bilal". Habawa! ai sai wuri yarude da gunguni na mamaki, idanu sukai zazzago baki a bude cikeda tambayoyi, ya mutumin da yakasa shuka iri na tsawon shekara zai zama Sarkinsu?. Bilal yadago kai a firgice, shin abin da kunnuwansa sukaji gaske ne ko Almara ko mafarki? Sarki ya sharesu yaci gaba da maganarsa kawai yana mai cewa. "Shekarar data wuce nabaku iri daban-daban a shuka a kawo min yau" yadan nisa can yaci gaba. "To amma baku sani ba DAFAFFEN IRI nabaku (wanda baya shuka) da kukaga yaki fitowa sai kuka canza da wani daban, Bilal kadai ne MAI GASKIYA da bai canzaba, yakawo min tukunya ba komai, dan haka kowa yayi gaisuwa ga sabon Sarki ku kwashe wadannan ciyayin kuban wuri". To masu karatu anan na kawo karshen wannan labari nawa. Ina. fata an fa'idantu da nishadantuwa, zan rufeda wannan hadisin dan sakon yafi shiga: Monzan Allah (S.A.W) yace: Gaskiya tanasa ayyuka nagari, ayyuka nagari suna kaiwa zuwa Aljanna. Mutum bazai gushe yana fadar gaskiya ba harsai an rubata shi a matsayin mai gaskiya awurin Allah. Karya na kaiwa zuwa ayyuka marasa kyau, wanda suke kai mutum wuta. Mutum bazai gushe yana karya ba harsai an rubuta shi Makaryaci a wurin Allah. "(Bkhr 8:116). Ubangiji Allah yabamu ikon fadin gaskiya dayin gaskiya. Ya tsaremu da fadin karya. www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 7


Darasi na 7

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA


***{Darasi na 7}***

Acikin bayani  hukunce hukuncen Sallah. Malam yace:

ﻛﺄﺣﻜﺎﻡ ﺍﻟﺼﻼﺓ
KA AHKAMIS SALLATI.
Ma'ana:
kamar hukunce hukuncen sallah.
BAYANI: Farkon kyakkyawan aikin da yake bin imani abaya
shine sanin hukunce-hukuncen Sallah.
Wato rukunan salla, farillan sallah, sunnoni da mustahabban sallah, da kuma abinda ya shafi sharadanta da abinda ke vatata.
Da kuma yin sallah kamar yadda Annabi (S.A.W) yakeyi ta hanyar cika ruku'u da sujjada da kuma
kyawun tsayuwa.
Kamar yadda sayyadi Abdullahi dan Abbas yake cewa: Ita cikakkiyar sallah itace wacce aka cikasa
ruku'unta da sujjadarta da kuma khushu'inta da duk wani ladubbanta, domin yin irin wannan sallar
itace zata hana mutun aikata alfasha da duk wani abin qi.
Kamar yadda Ubangiji yafada:
ﺇﻥ ﺍﻟﺼﻠﻮﺓﺗﻨﻬﻰ ﻋﻦ ﺍﻟﻔﺤﺸﺎ ﺀ ﻭﺍﻟﻤﻨﻜﺮ 0 ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﻌﻨﻜﺒﻮﺕ0
"ita dai sallah tana hana aikata alfasha da duk wani aikin munkari. WALLAHU A'ALAM. Sai gobe idan Allah (s.w.t) yakawo mu lokaci irin
wannan zamuci gaba.
Insha Allah. Allah ya karvi ibadunmu.

www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 5


Darasi na 5


DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

***{DARASI NA 5}***

Malam yace:
..... ﺗﺼﺤﻴﺢ ﺇﻳﻤﺎ ﻧﻪ
Ma'ana:
"Ya inganta imaninsa"
Bayani:
Imani a harshen larabci shine amincewa. Amma a Shari'ance shine gaskatawa da samuwar Allah madaukakin sarki.
Kamar yadda yazo acikin Alqur'ani mai girma:
ﻗﻮﻟﻮ ﺀﺍﻣﻨﺎﺑﺎﻟﻠﻪ ... ﺳﻮﺭﺓﺍﺑﻘﺮﺓ : ١٣٦
Ma'ana"kuce:
Munyi Imani da Allah (shi kadai)" Amma a wajen malamai cewa sukayi Imani shine
gaskatawa da Annabi Muhammad (S.A.W) a cikin dukkannin abinda yazo dashi daga wajan Allah (s.w.t). Malamai suka qara da cewa imani yana da rukunai
guda shida (6) kamar yadda Allah (s.w.t) ya fada:

ﻭﻟﻜﻦ ﺍﻟﺒﺮﻣﻦ ﺀﺍﻣﻦ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻷﺧﺮﻭﺍﻟﻤﻼﺀﻛﺔ ﻭﺍﻟﻜﺘﺐ
ﻭﺍﻟﻨﺒﻴﻴﻦ ...
Manzon Allah (s.a.w) yace: (Imani shine)
kabada gaskiya da Allah da Mala'ikunsa da littattafansa da Manzanninsa sannan kayi imani da Ranar Al-qiyama kuma kayi Imani da qaddara Al-
kairinta da sharrinta.
Imani yana daduwa da qaruwar ayyukan kirki,
kuma yana raguwa saboda aikata mummunan aiki
da savawa Allah.
Malamai suna kafa hujja da fadin Ubangiji (s.w.t) cewa: "sai Allah ya qarawa wadanda suka shiriya (wata)
shiriyar" ~suratu Maryam~ Da kuma inda yake cewa:
"wanne dayan kune wanda (Al-qur'ani) yaqara masa imani, to amma su wadanda sukayi imani sai
imanin ya qaru garesu"
ALLAH YA TSARE MANA IMANINMU.
Idan Allah yakaimu zamuci gaba.
Insha Allah.

www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 6


Darasi na 6

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

***{Darasi na 6}***

acikin bayanin

FARILLAH AINIH DA FARILLAH KIFAYA.

malam yaci gaba da cewa:

ﺛﻢ ﻣﻌﺮﻓﺔ ﻣﺎ ﻳﺼﻠﺢ ﺑﻪ ﻓﺮ ﺽ ﻋﻴﻨﻪ

SUMMA MA'ARIFATU MA YUSLEEH BIHI FARDHA AINIHY.
Ma'ana: "sannan yasan abinda zai gyara farinlan ainihinsa dashi".
... BAYANI....
Abinda ake nufi da Farillah ainih shine:
Duk wani aiki ko umarni da Allah (S.W.T) ya wajabtawa kowanne baligi mai hankali to yazo dashi shi da kansa. Shine aikin da wani bazai iya dauke masa shiba
wato kamar:

Sallah.
Azumi.
Zakka.
Hajji.
Umrah.
kalmar Shahada, da sauransu. Kamar yadda yazo acikin suratul- Asr " Ina rantsuwa da zamani haqiqah dan Adam yana cikin asara saidai wadanda sukayi imani suka kuma yi aiyuka masu kyau na kwarai".
FARILLA KIFAYA. Farillace wacce wani zai iya daukewa wani, misali: Wajibine kowa yazama likita, amma idan aka samu a gari wani yazama likita to ya daukewa sauran, sai dai kuma ayi qoqari wasuma su iya dan gaba. WALLAHU A'ALAM. Ina marhaba da duk wani qyara da za'ayi mini,kunsan dan adam akwaishi da kuskure. Allah ya bamu ikon sauke farillan dake kammu
Sai gobe zamuci gaba.
Insha Allah.

www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Tambaya ta 15.


Tambaya ta 15.


DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu alaikum.
Malam don ALLAH idan mutum yarasa raka'a biyu a sallar magriba ya zaiyi wurin ramasu ???

(daga Lukman Aminu)

          AMSA.
======================

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

Ga yadda zaiyi, wanda yasami raka'ar karshe ta sallar magriba, zai tashi yakawo raka'a daya, ya karanta fatina da sura a fili idan yakai raka'ar ba miqewa tsaye zaiyi ba, sai yayi zaman tahiya.
Sannan yasake tashi ya kuma kawo wata raka'ar itama ya karanta fatiha da sura a fili sannan idan
yakai raka'ar sai yayi sallama.

WALLAHU A'ALAM.

 www.hanyantsira.blogspot.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

tambaya


Shin Ya halatta mutum ya ajiye kare a gidansa ?

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum.
Malam wai ya halatta mutum ya a jiye kare a
gidansa ?

(Daga Zakari Sani).

AMSA:
__________________________


DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.


A'a Baya halatta, sai bisa ga lalura. Shari’a tayarda mutum ya iya ajiye kare don tsaron
gida, ko domin tsaron dabbobi a gona, ko domin farauta ta halas. Wadannan duka, sun halatta.
Amma inba haka ba, (wai ko dan sha’awa kawai) baya halatta.
Sannan a hakanma anfiso a killace masa wani waje nasa na musamman. Domin yazo a hadisi cewa:
Duk gidan da kare yake a cikinsa, mala’ikun Rahama basa shigarsa.
Wallahu A'alam.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 3


Darasi na 3

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA


LITTAFIN AHALARI

***{DARASI NA 3}***

....MUQADDIMA ~1~

Malam yace:
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ .

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM"
Dasunan Allah mai Rahma mai Jinqai.
.........BAYANI
"MUQADDIMA" wajene da malamai suke bayanin Abinda littafinsu ya qunsa, da dalilin da yasa sukayi littafin. Idan mukace "Malam yace" anan muna nufin abinda mawallafin littafin yafada. Malam yabude littafinsa da bismilla domin koyi da Al-qur'ani mai girma kuma da aiki da hadisin Shugaba (s.a.w) inda yake cewa: "Duk wani aiki daya zamo ma'abocin kima da daraja ba'a farashi da Bisimilla ba, toshi mai yankakkiyar albarkane. Ma'anar ALLAHU kuwa shine abinda halitta kaf
yakamata tariqeshi a matsayin abin bautarta da gaskiya, Kamar yadda Imamu Dahhaku yafada
Daga Sayyadi Abdullahi dan Abbas (r.a) yace: ALLAH (s.w.t) yafada acikin Al-qur'ani magirma
ﺍﻟﻠﻪ ﻻﺇﻟﻪ ﺇﻻﻫﻮﺍﻟﺤﻲ ﺍﻟﻘﻴﻮﻡ .
"ALLAHU LA'ILAHA ILLAHUWAL HAYYUL QAYYUM"
Ma'ana Allah dai shine Allah (daya cancanci a
bauta masa domin) babu wani Allah abin bautawa da gaskiya sai dai shi. Rayayyene shi wanda yake tsaye da zatinsa, da kuma rayuwar halitta gaba daya. Wallahu A'alam.
In Allah ya yarda zamuci gaba daga wajen da muka tsaya.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 2


Darasi na 2

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

LITTAFIN AHALARY
***{ DARASI NA 2 }***

Rasuwar mawallafin littafin.Wancan darasin mun tsaya akan tarihinsa, zamuci
gaba daga inda muka tsaya. Allah yayiwa mallam Abdulrahman Al-Akhdary rasuwa a wani kauye mai suna kujalo a shekara ta 953 amma wasu malaman sunce: Ya rasune a shekara ta 983 malamin yabarwa
almajiransa wasiyyar idan yarasu adaukeshi
akaishi garinsu wato (bandayosa) a binneshi acan kusa da gidansa. Hakan kuma akayi, muna fatan Allah (s.w.t) ya jiqansa ya gafarta masa, yabamu albarkacinsa.
Allah yadatar damu abisa bin Sunnar annabi (s.a.w).Darasi nagaba zamu shiga karatun littafin Insha
Allah.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

haqqin makotaka

Hakkin maqotaka.


DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalam Alaikum. Malam menene hukuncin wanda yahana makwabcinsa aron wani abu, wanda makwabcin ya tambaya alhali yana dashi ?

(Daga Idris Mustapha).

AMSA:-
_______________________________


ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.

A gaskiya ya sabawa Allah (S.W.T). Domin Allah (s.w.t) yace ka taimaki makwabcinka.
Hana makawabci taimako kuwa, alamar munafurci ne. Sannan da fadin Allah (s.w.t) acikin Al-qur'ani mai girma. “WA YAMNA’UNAL MA’UN”
(Suratul Ma’un aya ta 7). Saboda haka taimakon makwabci wajibine akan kowane musulmi.
WALLAHU A'ALAM.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like  

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

darasi na 1

Darasi na  1
LITTAFIN AHALARI

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

***{DARASI NA 1}***

Bismillahir rahmanir rahim. wasallallahu alan nabiyyil karim.
Kafin mushiga cikin littafin Akhdari zamu fara da TAQAITACCEN TARIHIN Mawallafin littafin wato "Abdurrahman Al-AKHDARI {R.A}. Sunansa Abdurrahman dan Muhammadus-Sagir dan Muhammad Amir Al-akhdari Amma anayi masa alkunya da Abi zaidin koda yake bai tava yin aure ba, amma abisa al'adar larabawa suna yiwa qananan yayansu alkunya da cewa baban wane ko
baban wance, tareda cewa qaramin yaro bashi da da, Kamar yanda Annabi Muhammad (s.a.w) da
dansa yayiwa Nana A'isha Alkunya da yaron daba ita ta haifaba, wato Abdullahi dan wajen yayarta Asma'u, sai yake kiranta da Ummu Abdullahi. Amma Imamu malik yana ganin makaruhine akira qaramin yaro da baban wane ko baban wance. An haifi malamin a wani qauyen Bandayosa dake qasar Algeria, a shekara ta 920, ya rubuta littafin
yana dan shekara Ashirin 20 a duniya.
Anayi masa laqabi da Al-akhdari ne saboda wata qabila da akece mata Akhdarar amma wasu malaman sun fadi wata ma'anar.
Zamuci gaba Insha Allah.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like  

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

tambaya

Tambaya ta 8.


DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA


Assalamu alaikum.
malam ina da wata 'yar uwa da aurenta yakare,kuma auren ya karene tana tsakiyar jinin al'adane,to malam zata irgane har dashi wannan jinin acikin IDDANTA KO YAYA ZATAYI ?


AMSA
**********************************

Eh zata fara Qirgen iddarta har da shi.
kuma akwai sabani mai karfi sosai a tsakanin malamai dangane da kansa sakin da akayi shi
alokacin da matar take cikin al'adarta. Imamai hudun nan masu mazhabobi sunyi ittifaki akan cewar sakin yayiwu duk da cewar sakin yazama na bidi'a kenan. Amma Ibnu Taymiyya da Ibnul Qayyim da wasu
almajiransu sunce: SAKIN BAI YIWU BA.
Har yanxu tana nan amatsayin matarsa.

WALLAHU A'AhLAM.

Dan Allah kudinga share dinsa ta facebook da whatsapp domin 'yan uwanku su amfana.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like  

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

koh kasan meyasa

KO KASAN MEYASA WANI LOKACI ZAKAJI KAMAN AN KIRA SUNANKA AMMA IDAN KAWAIGA SAI
KAGA BA WANDA YA KIRAKA ???


DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA

KO KASAN MEYASA WANI LOKACI ZAKAJI KAMAN AN KIRA SUNANKA AMMA IDAN KAWAIGA SAI
KAGA BA WANDA YA KIRAKA ???

Toga dalilin hakan.
Suhail (sahabi ne) yake cewa:Wata rana babansa ya aikesu banu haritha tare
dashi akwai wani mutumi wanda suke tafiya.Suna cikin tafiya sai suhail yaji kamar ankirasunansa acan baya.Yawaiga amma bai hango kowa ba.
Shima mutumin da suke tafiya tareda suhail shima yawaiga baiga kowa ba.
Bayan sundawo gida sai suhail yabawa babansa labarin abinda yafaru.
Sai baban suhail yace:
"Danasan zakaji irin wannan kiran shaidanun da ban aikekaba.Hadisin yana cikin Sahihul Muslim kitabud du'a,
hadith mai lamba 756.
Malamai sukace idan kaji irin wannan kira to
kada ka amsa musu domin shaidanu ne suke kiran sunanka kamar yadda wannan hadith ya tabbatar
mana.Ya Allah ka karemu daga sharrin shaidanu, kayi mana katangar karfe tsakanin mu dasu.


www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like  

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

labarin wani mutum

LABARIN WANI MUTUM DA MUTUWA TA RISKESHI.

dan uwa bani minti biyu ka daure ka/ki karanta.

DAGA  ZAUREN

HANYAN***TSIRA


ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

game da yadda wasu na gani suke cire sunan group da aka rubuta asalin post suna sana sa nasu su ji tsoron Allah su daina wannan ba abu bane mai kyau.


LABARIN WANI MUTUM DA MUTUWA TA RISKESHI.

Wani daga cikin magabata, wanda ma shiba musulmi bane. Dayazo mutuwa yasa aka kira masa manyan
sojojinsa sai yace musu, yanason su cikamar wasu wasiyoyi gudu uku, idan mai yanke kauna ta daukeshi. wato mutuwa a fayyace

Wasiyoyin kuwa sune kamar haka:

1. Likitocin da sukafi kowa kwareya a fadin kasarsa, su yakeso sudauki akwatin gawarsa sufito da'ita bainar jama'a kafin aje a binneshi.

2. Dukkan abin daya mallaka na kudi dana zinari ko azurfa, duk dukiyan sa yanason a tattarasu a watsasu a hanyar daza'a bi da gawarsa zuwa makabarta.

3. Hannayensa kuma yace yanason a barsu a wajen akwatin suna Lilo inda kowa dake wajen zai iya gani. Wani daga cikin sojojin nasa sai yayi mamakin wannan abun ya kasa rikewa saiya tambayeshi karin bayani shi
kuma sai yace:

1. Inason likitoci su dauki gawatane domin na nunawa mutane cewa yayinda mutuwa tazo ko da likitocin da sukafi kowa kwarewane, baza su iya warkadda mutum ba.

2. Inason a watsa dukiyata akan hanyane domin mutane susan cewa duk abinda aka samu a duniya, a duniya ake barinsa.

3. Inason abar hannayena suna rito ta wajene domin mutane su gane cewa munzo duniya hannu empty( ba komai)  haka kuma zamu koma hannunmu empty babu komai, bayan dukkan abinda muka mallaka na dukiya da sauran kayayyakin duniya bayan mungama cinye dukkan kwanakinmu a duniya,kuma wannan shine lokaci. Lokaci shine makiyinmu ba mutuwaba. To masu karatu kunjifa kafiri ma kenan yanayin tunani irin wannan, balantana mu Musulmai, masuyin Sallah.
Ya Allah Kasa muyi amfani da lokutanmu wajen neman lahira bana duniya kadaiba.
Allah ka jiqanmu ka gafarta mana.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like  

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

koh ka san meyasa??

KO KASAN MEYASA WANI LOKACI ZAKAJI KAMAN AN KIRA SUNANKA AMMA IDAN KAWAIGA SAI
KAGA BA WANDA YA KIRAKA ???


DAGA  ZAUREN

🕋HANYAN***TSIRA🕋

KO KASAN MEYASA WANI LOKACI ZAKAJI KAMAN AN KIRA SUNANKA AMMA IDAN KAWAIGA SAI
KAGA BA WANDA YA KIRAKA ???

Toga dalilin hakan.
Suhail (sahabi ne) yake cewa:Wata rana babansa ya aikesu banu haritha tare
dashi akwai wani mutumi wanda suke tafiya.Suna cikin tafiya sai suhail yaji kamar ankirasunansa acan baya.Yawaiga amma bai hango kowa ba.
Shima mutumin da suke tafiya tareda suhail shima yawaiga baiga kowa ba.
Bayan sundawo gida sai suhail yabawa babansa labarin abinda yafaru.
Sai baban suhail yace:
"Danasan zakaji irin wannan kiran shaidanun da ban aikekaba.Hadisin yana cikin Sahihul Muslim kitabud du'a,
hadith mai lamba 756.
Malamai sukace idan kaji irin wannan kira to
kada ka amsa musu domin shaidanu ne suke kiran sunanka kamar yadda wannan hadith ya tabbatar
mana.Ya Allah ka karemu daga sharrin shaidanu, kayi mana katangar karfe tsakanin mu dasu.


www.hanyantsira.mywapblog.com

📗📘
whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like   👇👇

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA TA 8

tambaya-da-amsa.jpg

Tambaya ta 8.


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA


Assalamu alaikum.
malam ina da wata 'yar uwa da aurenta yakare,kuma auren ya karene tana tsakiyar jinin al'adane,to malam zata irgane har dashi wannan jinin acikin IDDANTA KO YAYA ZATAYI ?


AMSA
********************************

Eh zata fara Qirgen iddarta har da shi.
kuma akwai sabani mai karfi sosai a tsakanin malamai dangane da kansa sakin da akayi shi
alokacin da matar take cikin al'adarta. Imamai hudun nan masu mazhabobi sunyi ittifaki akan cewar sakin yayiwu duk da cewar sakin yazama na bidi'a kenan. Amma Ibnu Taymiyya da Ibnul Qayyim da wasu
almajiransu sunce: SAKIN BAI YIWU BA.
Har yanxu tana nan amatsayin matarsa.

WALLAHU A'AhLAM.g

Dan Allah kudinga share dinsa ta facebook da whatsapp domin 'yan uwanku su amfana.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tamabyoyi.jpg

TAMBAYA

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Slm Malam dan ALLAH yahalatta mutumin da yake
da aure yaringa kallon film din BLUE FILM shi da matarsa ?

(Daga Aminu SBS)

AMSA
==========================

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

A'a bai halattaba, yin hakan haramunne, Allah (s.w.t) ya tsinewa mai kallon tsiraici da wanda
yake nunuwa.Akwai zunubi mai tarin girma, domin gudun kada mutum yafada zina yasa yayi aure, idan akace mutum yayi aure baya samun biyan bukata da
matarsa ta sunnah dole saiya kalli kafirai maqiya Allah da Manzonsa suna tafka masha'a suna aikata
zuna a fili yazama auren nasa bai katangeshi daga zina ba kenan.Duk ma'auratan da suka sabarwa kansu da irin
wannan muguwar dabi'ar tunda wuri sudaina. Bazasu ta6a samun biyan bukata ta wannan hanyar
ba. ABIN DAYA KAMATA SUYI SHINE:
=================
matsayinsu na ma'aurata su cire kunya su zauna
su tattauna tsakaninsu, akan shi mai gidan ko ita
uwar gidan wanne abu yafi so ko wanne abu tafiso tayi masa ko yayi mata a lokacin kwanciyarsu ta
aure ??? Wannan shine matakin daza su dauka amma maganar kallon B.f haramunne Allah (s.w.t) yana
fushi da ma'auratan da basa kishin junansu.
Da fatan ma'aurata zasu kiyaye. Allah ka aurar da matasanmu maza da mata su
huta da wannan bala'in albarkacin Muhammadu
Rasulullah (s.a.w).

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tambaya-da-amsa.jpg

TAMBAYA

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu alaikum mallam kamar yanda wasu suke fada a kwai wani hadisi da yake nuna cewa in dan mutum yayi sallam a baya alhali jam,i bai ciki ba bashida sallah mallam mene gaskiyar maganan

-AMSA-
*************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

hadisine ingantacce wanda yayi sallah a bayan sahu shi kadai bashi da sallah haka annabi (S.A.W) yace dan haka idan kazo masallaci bai kamata ka tsaya a bayan tsahu kai kadai ba sai se in sahun dake gabanka ya cika sai ka tsaya a bayan sahu kai kadai toh wannan babu laifi amma abinda ake magana shine ga sahu a gaba bai cika ba sai ka tsaya a baya ka fara sallah kaika dai har ka gama wani baizo kun hadu ba toh kai baka da sallah, wannan hadisin malamai sun masa fassarori daban daban kan maganganu guda uku na farko suke cewa wannan hadisin ya shafi koh wace irin sallah nafila da kuma ta farilla sannan wannan hadisin yana alauhumin babu yanda zakayi sallah a bayan sahu kai kadai yazo sallan ka ta inganta akwai masu wannan ra,ayin akwai kuma wayanda suke cewa da akwai wannan hukuncin amma an shafeshi amma zance mafi inganci wannan hukuncin yana nan tabbas cikin musulunci kuma idan mutum yayi sallah a bayan sahu shi kadai matukar a gabansa akwai wuri ya ki shiga dan ra,ayinsa toh bashi da sallah amna idan yazo ya samu waje ya cika bayan zaiyi ya samu sahu a gaba sai ya tsaya a baya yayi sallah shi kadai har aka gama sallah toh wannan sallarsa tayi saboda me saboda rashin kudura wajen ya shiga gaba dan gaban tarika ta cika kuma ka,ida sannaniya cikin shari,a shine duk abinda aka wajabta maka ana kallon abu guda biyu kafin wajibtin nan ya tabbatu akanka abu na farko ikon aiwatarwa abu na biyu kana sane da abun yayin da aka rasa hudura kaso kasamu waje sai ka kasa toh wannan kasawan ta sauke ma wajibtin yanzu wajibine ka shiga cikin sahu amma kazo sahun ya cika ba yanda za,ayi ka shiga kaga wajab cin shiga ya fadi idan ka tsaya baya kayi sallah toh sallah tayi kyau abu na biyu kuma dayakesa a sauke ma wajibci shine mantuwa ka tashi yin abu sai ka manta baza a kamaka da laifin cewa kakiyi ba koh da wajibine abun saboda mantuwa sai lokacin da ka tuna toh yanzu wajibcinsa ya hau kanka ALLAHU A,ALAM

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tamabyoyi.jpg

TAMBAYA

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Malam ina da tambayoyi guda biyu kamar haka:

{1}. Shin Malam ya halarta miji ya sanya hannu a cikin farjin matarsa a matsayin nau'i na biyan bukatarta da kuma kara mata jin dadi yayin saduwa ?

{2}. Shin akwai lokacin da (safe, rana,
yamma,dare), yafi cancanta miji ya sadu da matarsa abisa koyarwa ta sunnah ?

Allah ya Kara daukaka. Amin.
(Daga Sulaiman Muhammad Faisal).

AMSA
************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

1. Eh da zarar an daura aure atsakaninku, to
matarka ta zama halal agareka kanada damar taba ko ina asassan jikinta. Sannan dangane da sanyah hannu agabanta domin tayar da sha'awa alokacin saduwa, shima ya halatta. Mutukar dai yin hakan bazai kai izuwa ga
cutarwa agareta ba.

{2}. Eh ya halatta mutum yasadu da matarsa aduk
lokacin da sukaji sha'awar yin hakan.
Amma akwai wasu lokuta guda 3 mafiya dacewa wadanda Allah ya fadesu acikin Suratun nuur.Sune kamar haka:

{1}. Kafin Asubah.

{2}. Lokacin barcin Rana (wato Sanda ake tube sutura saboda zafin rana).

{3}. Bayan sallar Isha.
Wadannan loakatai su ake kira lokutan al'aura na muminai.
Don haka ma Allah ya umurcemu da cewar
kadamu kyale bayinmu da masu yimana hidima,
da Qananan yaranmu suna shigo mana batare da izini ba awadannan lokuta.
Wallahu a'alam.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tambaya-da-amsa.jpg

Tambaya


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA


Malam ina yawan wani mafarki wanda yake
tayarmin da hankali.
Sai naga a mafarkin ana nuna min TASHIN QIYAMA a zahiri.
Ana nuna min lallai tashin qiyama gaskiyane,nakanyi mafarkin exactly iri daya kullum innayi
baccin rana kuma nakan farka arazane a firgice cikin tashin hankali. Amma ban tabayin irin mafarkin da daddare ba ko
sau daya. Malam toh koh menene hakan.?
Nagode
(pls hide my id)


AMSA
********************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .


Shidai mafarki Kashi 2 ne.

{1}. Mafarki mai kyau wanda yake zuwa daga Allah
(swt).

{2}. MUMMUNAN MAFARKI wannan daga shaitan yake zuwa.(kamar yadda sahihan hadisai suka tabbatar).Shi Mafarkin da yake zuwa daga Allah din yarabu
zuwa kashi 3.

{1}. Yakan zo ta fuskar Umurni ko hani (kamar
mafarkin Annabawa kenan (a.s).

{2}. Yakan zo da bushara... Kamar ka ganka a aljannah, ko ka ganka cikin Koshin lafiya, etc.

{3}. Yakan zo da Gargadi.. Kamar irin wannan naka din kenan. Saboda haka mafarkin ganin tashin alkiyamah,kuma acikin Tashin hankali, WANNAN GARGADI
AKEYI MAKA. Ina baka shawarar cewa ka gyara halayenka da
dabi'unka. Kuma idan kana da iyaye araye, to wajibi ne kaje ka gyara dangan takarka dasu.
Idan kuma akwai abinda kasan kana aikatawa aboye, to LALLAI KAYI KOKARI KA DENA!!

Allah y shiyemu baki daya.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tamabyoyi.jpg

TAMBAYA


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Salamu alaykum.
Malam tambayata anan shine; idan mutum yanada alwala saiya sumbaci matarsa (kissing dinta), alwalarsa ta karye ? Kuma meye mafita?.

(Daga:SUNUSI SANI ALASSAN KAFIN MAIYAKI).


AMSA
*******************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .


Hadisi ya inganta daga Sayyidah AISHA (RTA)
cewa: "MANZON ALLAH (S.A.W) IDAN YAGAMA ALWALA
YAKAN SUMBANCI WATA DAGA CIKIN MATANSA, SANNAN YAFITA ZUWA SALLAH BA TARE DAYA SAKE ALWALA BA"
(Abu dawud, nisa'eey suka ruwaito shi)

Dangane da wannan mas'alar akwai maganganu
guda uku da malamai sukayi. SHAFI'IYYAH SUNCE Shafar mace ko kissing yana karya alwala kai tsaye.
MALIKIYYAH DA HANBALIYYA SUNCE:
Alwalarsa bata karyeba, saidai in yayine da niyyar sha'awa.

HANAFIYYA SUNCE:
Alwalarsa bata karye ba saidai in wani abu yafito daga gabansa.

WALLAHU A'ALAM.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tamabyoyi.jpg

TAMBAYA

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Slm Malam dan ALLAH yahalatta mutumin da yake
da aure yaringa kallon film din BLUE FILM shi da matarsa ?

(Daga Aminu SBS)

AMSA
==========================

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

A'a bai halattaba, yin hakan haramunne, Allah (s.w.t) ya tsinewa mai kallon tsiraici da wanda
yake nunuwa.Akwai zunubi mai tarin girma, domin gudun kada mutum yafada zina yasa yayi aure, idan akace mutum yayi aure baya samun biyan bukata da
matarsa ta sunnah dole saiya kalli kafirai maqiya Allah da Manzonsa suna tafka masha'a suna aikata
zuna a fili yazama auren nasa bai katangeshi daga zina ba kenan.Duk ma'auratan da suka sabarwa kansu da irin
wannan muguwar dabi'ar tunda wuri sudaina. Bazasu ta6a samun biyan bukata ta wannan hanyar
ba. ABIN DAYA KAMATA SUYI SHINE:
=================
matsayinsu na ma'aurata su cire kunya su zauna
su tattauna tsakaninsu, akan shi mai gidan ko ita
uwar gidan wanne abu yafi so ko wanne abu tafiso tayi masa ko yayi mata a lokacin kwanciyarsu ta
aure ??? Wannan shine matakin daza su dauka amma maganar kallon B.f haramunne Allah (s.w.t) yana
fushi da ma'auratan da basa kishin junansu.
Da fatan ma'aurata zasu kiyaye. Allah ka aurar da matasanmu maza da mata su
huta da wannan bala'in albarkacin Muhammadu
Rasulullah (s.a.w).

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tambaya-da-amsa.jpg

TAMBAYA

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu alaikum mallam kamar yanda wasu suke fada a kwai wani hadisi da yake nuna cewa in dan mutum yayi sallam a baya alhali jam,i bai ciki ba bashida sallah mallam mene gaskiyar maganan

-AMSA-
*************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

hadisine ingantacce wanda yayi sallah a bayan sahu shi kadai bashi da sallah haka annabi (S.A.W) yace dan haka idan kazo masallaci bai kamata ka tsaya a bayan tsahu kai kadai ba sai se in sahun dake gabanka ya cika sai ka tsaya a bayan sahu kai kadai toh wannan babu laifi amma abinda ake magana shine ga sahu a gaba bai cika ba sai ka tsaya a baya ka fara sallah kaika dai har ka gama wani baizo kun hadu ba toh kai baka da sallah, wannan hadisin malamai sun masa fassarori daban daban kan maganganu guda uku na farko suke cewa wannan hadisin ya shafi koh wace irin sallah nafila da kuma ta farilla sannan wannan hadisin yana alauhumin babu yanda zakayi sallah a bayan sahu kai kadai yazo sallan ka ta inganta akwai masu wannan ra,ayin akwai kuma wayanda suke cewa da akwai wannan hukuncin amma an shafeshi amma zance mafi inganci wannan hukuncin yana nan tabbas cikin musulunci kuma idan mutum yayi sallah a bayan sahu shi kadai matukar a gabansa akwai wuri ya ki shiga dan ra,ayinsa toh bashi da sallah amna idan yazo ya samu waje ya cika bayan zaiyi ya samu sahu a gaba sai ya tsaya a baya yayi sallah shi kadai har aka gama sallah toh wannan sallarsa tayi saboda me saboda rashin kudura wajen ya shiga gaba dan gaban tarika ta cika kuma ka,ida sannaniya cikin shari,a shine duk abinda aka wajabta maka ana kallon abu guda biyu kafin wajibtin nan ya tabbatu akanka abu na farko ikon aiwatarwa abu na biyu kana sane da abun yayin da aka rasa hudura kaso kasamu waje sai ka kasa toh wannan kasawan ta sauke ma wajibtin yanzu wajibine ka shiga cikin sahu amma kazo sahun ya cika ba yanda za,ayi ka shiga kaga wajab cin shiga ya fadi idan ka tsaya baya kayi sallah toh sallah tayi kyau abu na biyu kuma dayakesa a sauke ma wajibci shine mantuwa ka tashi yin abu sai ka manta baza a kamaka da laifin cewa kakiyi ba koh da wajibine abun saboda mantuwa sai lokacin da ka tuna toh yanzu wajibcinsa ya hau kanka ALLAHU A,ALAM

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

TAMBAYA

tamabyoyi.jpg

TAMBAYOYI

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Malam ina da tambayoyi guda biyu kamar haka:

{1}. Shin Malam ya halarta miji ya sanya hannu a cikin farjin matarsa a matsayin nau'i na biyan bukatarta da kuma kara mata jin dadi yayin saduwa ?

{2}. Shin akwai lokacin da (safe, rana,
yamma,dare), yafi cancanta miji ya sadu da matarsa abisa koyarwa ta sunnah ?

Allah ya Kara daukaka. Amin.
(Daga Sulaiman Muhammad Faisal).

AMSA
************************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

1. Eh da zarar an daura aure atsakaninku, to
matarka ta zama halal agareka kanada damar taba ko ina asassan jikinta. Sannan dangane da sanya hannu agabanta domin tayar da sha'awa alokacin saduwa, shima ya halatta. Mutukar dai yin hakan bazai kai izuwa ga
cutarwa agareta ba.

{2}. Eh ya halatta mutum yasadu da matarsa aduk
lokacin da sukaji sha'awar yin hakan.
Amma akwai wasu lokuta guda 3 mafiya dacewa wadanda Allah ya fadesu acikin Suratun nuur.Sune kamar haka:

{1}. Kafin Asubah.

{2}. Lokacin barcin Rana (wato Sanda ake tube sutura saboda zafin rana).

{3}. Bayan sallar Isha.
Wadannan loakatai su ake kira lokutan al'aura na muminai.
Don haka ma Allah ya umurcemu da cewar
kadamu kyale bayinmu da masu yimana hidima,
da Qananan yaranmu suna shigo mana batare da izini ba awadannan lokuta.
Wallahu a'alam.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

yadda ake warware sihiri a musulunci

YADDA AKE WARWARE SIHIRI


TAMBAYA:

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu alaikum.
Dan Allah malam a fitar dani daga cikin duhu gameda abin da yake damuna. Mahaifiya tace taje gurin Boka ayi mata maganin ciwon mara da yake damunta, tace tana da ciki yakai shekara guda da rabi, amma likitoci sunyi scanning sunce ba komai tosai Bokan yace mata asiri akayi mata, kuma zaiyi mata magani nan take ta haife abinda yake cikinta amma zata kawo tunkiya da dubu bakwai, sai take min magana in kawo kudi a sayi tunkiyar kuma akai masa dubu bakwan, to gaskiya malam zuciyata bata aminta da Bokan bane. Shiyasa Nakeso kabani fatawa shin irin wannan hanyar ta magani ta halatta a addini ? Idan bata halatta ba wacce hanya zanbi wajen qin biyan kudin da kuma sanar da ita ? Wassalam nagode malam Allah yaqara basira.

(Daga Binta Umar).

AMSA
------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
To ‘yar uwa, tabbas ba'a warware sihiri ta hanyar sihiri, saidai ana iya warware sihiri ta hanyar ayoyin
Alqur’ani. Wasu malaman sunyi bayani cewa:Ana iya warware sihiri ta hanyar karanta wadannan ayoyi kamar haka:

1- Ayatul-Kursiyyu.
2- Quliya.
3- Ikhlas.
4- Falaki da Nasi.
5- Sai kuma ayah ta: 117 zuwata 122, cikin Suratul
A’araf.
6- Sai kuma Ayah ta: 79-81 cikin Suratu Yunus.
7- Sannan sai Ayah ta: 65-70 cikin Suratu Dhaha.Za’a karanta su, sai a tofa a ruwan da aka zuba magarya guda bakwai, sannan ayi wanka dashi a waje mai tsafta.Haka ake magance sihiri cikin yardar Allah. Bai halatta ki taimaka mataba, wajan bada
wadannan kayan da boka yanema duk da cewa mahaifiyarkice.
Saboda ba’a yiwa iyaye biyayya a wajen sabon Allah.Ya wajabta gareki kayi mata nasiha cikin hikima,kisanar da ita cewa:Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:“Duk wanda yaje wajan boka, ya tambaye shi wani
abu, Allah bazai amshi sallarsa ba, ta kawana
arba’in”Muslim ya rawaito acikin hadisi mai lamba ta:2230. Kinga idan mutum ya mutu acikin wadannan
kwanaki akwai matsala, musamman ma tun da akwai hanyar da shari’a ta yarda da ita.Sannan awani hadisin kuma yana cewa:“Duk wanda yaje wajan boka ya gaskata abin daya fada, to tabbas ya kafurce da abinda Annabi Muhammad yazo dashi”Kuduba Sunanu-Abi-Dawud hadisi mai lamba ta:
3904, kuma Albani ya inganta shi.INA GANIN DA IRIN WADANNAN HADISAN ZAKI IYA
GANAR DA ITA, TA DAWO KAN HANYA. Allah Shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

ZUCIYATA

tamabyoyi.jpg

Malam zuciyata tanason aikata sa6o, yaya zanyi
na hanata ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Salam, malam a cikin zuciya ta ina jin tsoron Allah,kuma ina son bin umarnin Allah, saidai ina yawan sa’bon Allah kuma, malam inaso a taimake ni da shawara akan hakan ?

(Daga sadis Auwal).

AMSA:
-------------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan uwa, ina fatan zaka karanta wannan ‘kissar
da idon basira, domin zaka sami shawarar da kake bukata gata kamar haka:

Wata rana wani saurayi yaje wajen Ibrahim ‘dan Adhama, (‘daya daga cikin magabata), sai yace
masa zuciyata tana tunkuda ni zuwa sa’bo, kayi min wa’azi. Sai ya ce masa:“Idan ta kirawo ka zuwa sa’bawa Allah to ka saba masa, amma da sharuda guda biyar.
Sai saurayin ya ce fadi mujisu Sai yace:

1. Idan zaka sabawa Allah, to kabuya a wurin da bazai ganka ba, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, yaya za’ayi na boye masa, alhalin babu abin da yake ‘buya gareshi ???Sai yace:Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kuma yana ganinka.

2. Idan zaka sabawa Allah to karka saba masa acikin kasarsa, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina zanje, alhali duka duniya tasace ???Sai yace masa:
Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kana zaune a saman kasarsa ?

3. Idan zaka sabawa Allah to kadaina cin arzikinsa.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah, ta yaya zan rayu alhali duka ni’imomi daga gareshi suke ?Sai yace masa:
Yanzu ba kajin kunya ka sa’ba masa alhali yana ciyar da kai kuma Yana shayar dakai, Yana baka
karfi.

4. Idan ka sabawa Allah, to idan mala’iku sukazo tafiya dakai Wuta, kace bazaka tafi ba Aljanna za ka.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah ai sunfi ‘karfina, korani
zasuyi.

5. Idan ka karanta zunubanka a takardarka ranar
alkiyama kace ba kaine ka aikata suba.
Sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina mala’iku masu kiyayewa, sai yafashe da kuka yatafi yana maimaita
wannan Kalmar ta karshe.IN HAR KANA TUNA ‘DAYA DAGA CIKIN WADANNAN IDAN ZAKA AIKATA ZUNUBI, TO TABBAS ZAKAJI KUNYAR ALLAH.Tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki.
Ya Allah ka tsarkake mana zukatanmu daga sabo.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

LIMAMIN MU YA MANTA AYA A SALLAH

tambaya-da-amsa.jpg

LIMAMINMU YA MANTA AYA DAYA A FATIHA ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

LIMAMINMU YA MANTA AYA DAYA A FATIHA ?

Assalamu alaikum, malam barka da qoqari.Mal. Ya matsayin sallar da liman ya tsallake aya
guda a cikin fatiha ???
Jazakallah.
(Daga Halliru abdullahi)

AMSA.

=======================

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan'uwa Annabi (s.a.w) yana cewa:"Babu sallah ga wanda bai karanta fatiha ba"kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta:723.Malamai sunyi sabani akan Idan liman ya manta
aya daya a Fatiha, a sallar da take ta farilla, bai tuna ba, sai bayan yayi sallama, wasu malamai sukace zaiyi sujjadar rafkannuwa.
Amma zance mafi inganci shine:Idan har ba'a samu lokaci mai tsawo ba, to sai yatashi yasake raka'a daya.Idan kuwa an samu tazara mai tsawo tsakanin
lokacin daya tuna da kuma lokacin sallamarsa, to
zai sake sallar ne gaba dayanta, saboda fatiha
rukuni ce ta sallah bata tsayawa sai da ita, kamar yadda hadisin daya gabata yake nuni.Domin neman Qarin bayani sai aduba Fatawaa
Alajna Adda'ima:5/331.
Allah shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

MUTANE UKU ALLAH BA ZAI MUSU RAHAMA BA

tunatarwa.jpg

Mutane 3 Allah bazai yi musu rahmaba.

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

MUTANE UKU ALLAH YA HARAMTA MUSU SHIGA ALJANNAH
Manzon Allah (SAW) Yace:"Mutane uku Allah ya haramta musu shiga Aljannah.

1. Wanda ya dawwama yana shan giya.

2. Da mai wulakanta iyayensa.

3. Da wanda yake barin Iyalansa suna aikata Fasadi.

[Nasa'I, Hakim, Bazzar, Ahmad].

Ya Allah ka tsaratar damu daga fushinka.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

MANYA MANYAN AIYUKAN ZUNUBAI

tamabyoyi.jpg

Manya Manyan Aiyyukan Zunubi

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

WADANNE AYYUKANE SUKAFI KOWANNE AIKI GIRMAN ZUNUBI ?

Abdullahi dan Mas'ud yace:Wata rana na tambayi Manzon Allah (S.A.W) nace:Ya Manzon Allah a Duk cikin laifukan da ake yiwa Allah wane laifi ne yafi kowane laifi girman Zunubi a wajan Allah (s.w.t) ?Sai Manzon Allah (S.A.W) yace:

1. Ka sanya wa Allah kishiya (Shirka) Alhalin Shi ya halicce ka shi kadai. Sai Abdullahi dan Mas'ud yace tabbas wannan
babban al'amari ne.
Sai kuma me?

2. Manzon Allah (S.A.W) yace:Ka kashe danka don kar yaci abinci tare dakai a
rayuwa, dan kar kadauki da wainiyarsa.
Sai Abdullahi yace:
Sai kuma me?

3. Manzon Allah (S.A.W) yace:Kayi Zina da matar makwafcin ka.Yan Uwa kunji a duk cikin laifukan da yafi girman zunubi a wajen Allah bayan shirka.Bayan ita sai Kisan kai, ba wani laifi da ya kai lafin
Zina a musulunci girman zunubi.
Duk wanda ya dauki zina amatsayin sana'a, ko a matsayin aikin yi toh Wallahi ya gaiyato fushin Allah akan sa, kuma yana sone ya jefa Al'umma acikin masifa cikin bala'i, kuma zai gamu da
masifu, zai gamu da bala'i zai gamu da walakanci tun a duniya kuma zaiyi mum munan karshe, a
lahira kuma zai gamu da azaba mafi muni.
Allah ya kare mu daga aikata wadan nan manyan laifuka, ya kuma karemu daga sharrin shaidan,Allah ya shiryemu baki daya.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

gurare da aka haramta wa maxe ta kalla a jikin yar uwanta mace

tambaya-da-amsa.jpg

Wadanne gurarene aka Haramta mace takalla ajikin 'yar uwarta mce ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

Malam menene hukuncin mace tabayar da jikinta
ga mata yan’uwanta don ayi mata wanka saboda kwalliya ko irin dilka da halawa din nan wai haramunne Koda ta rufe mamanta da mazaunanta ?Idan haramun ne kenan daga ina zuwa inane
tsiraicin mace da bai kamata yar’uwarta mace ta gani ba ?
Jazakallahu khairaljazaaa.
(Daga Murjanat Sunusi).

AMSA
-------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To ‘yar uwa malamai sunyi sabani gameda tsaraicin mace ga ‘yar’uwarta musulma.

Akwai wadanda suka tafi akan cewa:

1- Bai halatta ‘yar uwarta mace taga wani abu a jikinta ba, sai abin daya saba bayyana a tsakanin
mata.Idan suna zaune isu-isu, kamar kafa da hannu da fuska da wuya da makamacin haka.

2. Saidai abin da mafi yawan malaman fiqhu suka tafi akai shine:
Al’aurar mace ga ‘yar uwarta musulma tana farawa ne daga cibiya zuwa guiwa, kamar yadda al’aurar maza take a tsakaninsu.
Don haka bai hallata tabari wata mace takalli samada wannan wurin da aka iyakance ba.

3. Amma idan kafira ce matar to malamai sunyi bayani cewa bazata kalli wani abuba, sai abin da
yasaba bayyana, don haka sai a kula lokacin da za’aje dilka wajan wacce ba musulma ba, don kada garin neman gira a rasa ido .
Sannan a bisa wannan bayanin da kikayi, dilkar da kika siffanta zata zama bata halatta ba, tunda za’a
ga abin da shari’a bata hallatata a gani ba.
WALLAHU A'ALAM

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

shaawar boye...

tunatarwa.jpg

Sha'awar 6oye

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Wata rana Wani Sahabin Manzon ALLAH (S.A.W)
Mai Suna Shaddad Bin Aus (R.A), Yafashe Da
Kuka.Sai Aka Tambaye Shi Dalilin Yin Kukan nasa.Sai YaCe:-
"Wani Abu Ne, Da Naji Daga Manzon ALLAH
(S.A.W) Na Tuna, Shi Yasani Kuka.NaJi Manzon ALLAH (S.A.W) Yana Cewa:
Ina Jiwa Al'ummata Tsoron SHIRKA Da Sha'awar boye)"Sai Nace:"Ya RASULULLAHI (S.A .W)! Al'ummarka Zatati
Shirka a Bayanka???
Sai YaCe:"E! Amma Bazasu Taba Bautawa Rana Ko Wata Ko
Dutse Ko Gunki Ba.
Sai Dai Zasu Riqa Yin RIYA Da Ayyukansu.

2. Sha'awar Boye Kuma, Dayansu Sai Yawayi Gari Yana Mai Azumi.Sai Wata Sha'awa Daga Sha'awoyinsa Ta Bijiro
Masa, Sai Ya Bar Azumin Nasa (ma'ana ya karya azumin).(Imam Baihaqi Ya RuwaitoShi a Cikin Shu'abul-
Iman).HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKEEL!WANNAN SHINE HALIN DA YAWANCIN MUSULMI A YAU SUKA TSINCI KANSU.YA ALLAH KA TSERATAR DAMU DAGA WANNAN
BALA'I MAICI BAL-BAL KAMAR WUTAR DAJI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Tambaya na 1...

tamabyoyi.jpg

Tambaya ta 1


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum.
Malam dan Allah a boye sunana:Nice ina tare da saurayina amman ba'a gari daya
muke ba, kusan kullun muna waya amman sai yanemi muyi sabon Allah.wato mu makin imagination muna sex da juna.
(i.e masturbation).
kuma nayi ta mishi wa'azi amman kullum abun karuwa yakeyi.
Mallam matsalar itace da farko da muka hadu a lokacin I dnt knw his character saina mishi
alkawarin bazan barshi ba, zan aure shi, kuma yanzu har ga Allah na canza ra'ayi akansa saboda halayen sa.Shin mallam idan na rabu dashi menene hunkucin alkawarin danayi ?

(Daga wata baiwar Allah).

AMSA
**************************

Allah yasaka miki da alkhairi.
kuma Allah ya Qara miki tsoron ALLAH afili da boye.Tabbas irin wadannan abubuwan da kikace saurayinki yana umurtarki dasu, suna daga cikin hanyoyin da shaidanun samari sukebi domin lalata
'ya'yan mutane.Ai kinyi masa alkawarine abisa zatonki cewar shi mutumin kirkine irin wanda kowacce mace takeso ta aura.Amma tunda halayensa sun nuna cewar shi shaydani ne, kuma mai neman lalata, wato irin
namijin da kowacce mace mai addini take QIN ta aura, to tabbas yazama WAJIBI ki Qaurace masa.
(kamar yadda Malam MAI AHALARI ya fada).
Kiqara godewa Allah tunda ya tsareki daga bin ra'ayin wannan shaydanin kuma kyawun fuska ko
dukiya ko zaqin bakinsa bai rudeki ba.
**Allah yana cewa:
"KARKU KARKATA IZUWA WADANNAN DA SUKA ZALUNCI KANSU, SAI WUTA TAQONA KU"
Malamai sukace:
DUK WATA ALAQAR DA BA'A QULLA TA DOMIN ALLAH BA, TO MUSIBACE QARSHENTA"Allah ya kiyaye.Yadda kika soshi tunda farko domin Allah, to yanzunma KI RABU DASHI DOMIN ALLAH.
zaki samu lada mai yawa awajen Allah.
domin Allah yanason masu yin soyayya ko kiyayya dominsa.
Kici gaba da addu'a. INSHA ALLAHU zaki samu wanda yafishi.
WALLAHU A'ALAM.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

zuciyata tana son aikata sabo

tambaya-da-amsa.jpg

Malam zuciyata tanason aikata sa6o, yaya zanyi
na hanata ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Salam, malam a cikin zuciya ta ina jin tsoron Allah,kuma ina son bin umarnin Allah, saidai ina yawan sa’bon Allah kuma, malam inaso a taimake ni da shawara akan hakan ?

(Daga sadis Auwal).

AMSA:
-------------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan uwa, ina fatan zaka karanta wannan ‘kissar
da idon basira, domin zaka sami shawarar da kake bukata gata kamar haka:

Wata rana wani saurayi yaje wajen Ibrahim ‘dan Adhama, (‘daya daga cikin magabata), sai yace
masa zuciyata tana tunkuda ni zuwa sa’bo, kayi min wa’azi. Sai ya ce masa:“Idan ta kirawo ka zuwa sa’bawa Allah to ka saba masa, amma da sharuda guda biyar.
Sai saurayin ya ce fadi mujisu Sai yace:

1. Idan zaka sabawa Allah, to kabuya a wurin da bazai ganka ba, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, yaya za’ayi na boye masa, alhalin babu abin da yake ‘buya gareshi ???Sai yace:Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kuma yana ganinka.

2. Idan zaka sabawa Allah to karka saba masa acikin kasarsa, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina zanje, alhali duka duniya tasace ???Sai yace masa:
Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kana zaune a saman kasarsa ?

3. Idan zaka sabawa Allah to kadaina cin arzikinsa.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah, ta yaya zan rayu alhali duka ni’imomi daga gareshi suke ?Sai yace masa:
Yanzu ba kajin kunya ka sa’ba masa alhali yana ciyar da kai kuma Yana shayar dakai, Yana baka
karfi.

4. Idan ka sabawa Allah, to idan mala’iku sukazo tafiya dakai Wuta, kace bazaka tafi ba Aljanna za ka.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah ai sunfi ‘karfina, korani
zasuyi.

5. Idan ka karanta zunubanka a takardarka ranar
alkiyama kace ba kaine ka aikata suba.
Sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina mala’iku masu kiyayewa, sai yafashe da kuka yatafi yana maimaita
wannan Kalmar ta karshe.IN HAR KANA TUNA ‘DAYA DAGA CIKIN WADANNAN IDAN ZAKA AIKATA ZUNUBI, TO TABBAS ZAKAJI KUNYAR ALLAH.Tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki.
Ya Allah ka tsarkake mana zukatanmu daga sabo.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

shin akwai idda a kaina?

tamabyoyi.jpg

Shin akwai IDDA akaina ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum.
Malam mutum ne yanada mata, sun haihu tare da
ita ‘ya’ya hudu sai ya saketa, Sai wani ya aure ta.Suna tare da shi, sai suka sami ‘ya’ya guda biyu
(2).To, wannan mijin na farko, mai ‘ya’ya hudu (4) sai
ya mutu.Sai matar take cewa “Zata fito taje gidan wancan
(mamacin) tayi IDDAH.
Yaya wannan al’amarin yakene ?

(Daga Umar Hafiz)

AMSA:

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

-------------------------------------
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Babu abin daya hadata da wancan mamacin gameda takaba ko IDDAH. Wadannan ‘ya’yan nasu guda hudu wadanda sune
ainihin ‘ya’yan mamacin zasu tafi domin suci gado.
Amma ita kuwa babu ruwanta da wani abu nasa tunda sun rabu tun kafin ya rasu.
ALLAH SHINE MASANI.

www.hanyantsira.mywapblog.com

whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

gyaran zuciya

tunatarwa.jpg

Domin gyaran zuciya


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamun alaikum.
Allah yagafarta malam, wadanne abubuwane zanyi
domin gyara zuciyata da imanina ?Bissalam.

(daga Aminatu Farouk)

AMSA
*********************

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

Hakika wannan tambayar tanada muhimmanci
sosai.Kuma tabbas babu wani abinda yake gyara zuciyar Mumini face ambaton Allah (s.w.t).Allah (s.w.t) yana cewa:''KUYI SANI CEWAR DA AMBATON ALLAH NE ZUCIYA TAKE SAMUN NUTSUWA''Zikirin Allah (SWT) shine babban abinda yake raya zuciyar mumini kamar yadda Manzon Allah (s.a.w) yake cewa:"MISALIN WANDA YAKE ZIKIRIN ALLAH DA WANDA
BAYAYI, KAMAR MISALIN RAYAYYE NE DA MATACCE".
(bukhary da Muslim).
Babu abinda yake Katangewa zuciyar Mumini daga sharrin Shaitan face zikirin Allah (swt).Shugaba (s.a.w) yana cewa:
"HAKIKA MISALIN WANNAN (DA YAKE ZIKIRIN ALLAH), KAMAR MISALIN MUTUMIN DA MAQIYA (ABOKAN GABA) SUKA KOROSHI AGUJE, HAR SAI DAYA ISO WATA KATANGA MAI QARFI, YA SHIGA YA TSARE KANSA DAGA GARESU.HAKANAN BAWA BAZAI IYA TSARE KANSA DAGA
SHAITAN BA, SAIDA ZIKIRIN ALLAH"(tirmizy ne ya ruwaitoshi akan hadisi mai lamba 2,863).Sannan babu abinda yafi tseratar da mutum daga azabar Allah, kamar zikirin Allah.Manzon Allah (s.a.w) yana cewa:
"BABU WANI AIKIN DAYAFI TSERATAR DA BIL-ADAMA DAGA AZABAR ALLAH, KAMAR ZIKIRIN
ALLAH (azza wa jalla)."(Imamu Malik ya ruwaitoshi acikin Muwatta' juz'i na 1 shafi na 211 hadisi na 492.Da kuma Imamu Ahmad acikin Musnad juz'i na 5, shafi na 293, hadisi mai lamba 22,132).Babu abinda yake gyara imanin 'Dan Adam kamar ilimi da kuma aiki dashi..
Don haka munemi ilimin addini mai amfani.Kuma muji tsoron Allah. Mu aikata ayyuka na
kwarai.Allah ka shiryar damu akan tafarki madaidaici.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

mace mai ciki

tambaya-da-amsa.jpg

Shin malam ko ya halatta mace mai ciki ta daina sallah ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum
Dafatan malam yawuni lafiya.Malam don allah inaso akara mana haske akan
mene hukuncin matar datake zargin mijinta ?
Sannan malam shin ya halasta mace mai juna biyu ta daina sallah ?
Nagode.

(Daga Fateemah Muhammad).

AMSA
---------------------------------------


ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Shi Musulunci addini ne wanda ya gina al'ummarsa abisa kyautata mu'amala da yarda da juna da amincewa da kare mutuncin juna.Don hakane ma Musulunci baya yarda da duk
abinda ya zamto zargi ne, wato babu Qwararan shaidu wadanda suka tabbatar da faruwa ko
kasantuwar abin.Abinda kike zargin mijinki dashi, duk dadai ke zuciyarkita yardar miki cewar yana aikata wannan abin, to amma bakki da Qwakwarar Shaidar da zata tabbatar da zarginda kike yi masa.Yazama wajibi kicire zargi a zamanku na auratayya.

2. AMSAR TAMBAYA TA BIYU.Ba'a daukewa mai ciki sallah yazama wajibi ta kawota.Akwai aiyuka da dama na addini da ake daukewa
dan adam idan larura irin wannan tafaru akansa,amma ita sallah koda kana kwance baka iya tashi
muddin kasan a inda kake saika kawota koda jingina a bango ne.Balantana mace mai ciki wacce har takanyi wanke-wanke shara etc.Saboda haka 'yan uwa mudaina sakaci da sallah.
ALLAH SHINE MASANI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

makomar dan kafiri jinjiri

tamabyoyi.jpg

Malam menene makomar dan kafiri jariri idan ya mutu ???

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum
Malam menene makomar dan kafiri jariri idan ya
mutu ???Wai da gaske dan Al-jannah ne ???
Allah yakarawa malam lafiya.

(Daga Hafiz Lukhman).

AMSA
-----------------------------------------------


ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To malamai sunyi sabani akan yadda za’ayi da ‘ya’yan kafirai zuwa maganganu:

1. Allah zai sakasu a Aljanna, saboda basuyi aikin da Allah zaiyi musu azaba ba.

2. Akwai malaman da sukace za’ayi musu
jarrabawa ranar alkiyama.

3. Akwai wadanda suka tafi akan mayar da lamarinsu zuwa ga Allah, kada ayi musu shaida da wuta ko Aljanna, saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi.
“Allah ne ya san abin da sukayi nufin aikatawa”.kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai
lamba ta: 1384.

4. Akwai malaman da suka tafi akan cewa:
‘Yan wuta ne.Sai dai babban malamin nan Ibnul-kayyim ya rinjayar da Magana ta farko, wato suna Aljanna,saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gareshi.
“Kowanne abin haihuwa ana haihiuwarsa ne akan
musulunci, iyayansa ne suke zamar dashi
bayahude ko banasare”Kuduba Sahihul Bukhari hadisi mai lamba ta :1385.
Su kuma gashi sun mutu suna yara kaga suna nan akan musuluncinsu.Sannan Allah yana cewa:“Bamu kasance munayin azaba ba, harsai mun aiko manzo” (Suratul Isra’i aya ta: 15).kaga su kuma basu balaga ba, balle su fahimci
abinda mazanni sukazo dashi, sannan kuma suba azzalumai bane, azabar Allah kuma tana tabbata ne
ga azzalumai.Don neman Karin bayan kuduba:(Darikul hijratain :387).Allah Shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

zuciyata tana son aikata sabo

tambaya-da-amsa.jpg

Malam zuciyata tanason aikata sa6o, yaya zanyi
na hanata ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Salam, malam a cikin zuciya ta ina jin tsoron Allah,kuma ina son bin umarnin Allah, saidai ina yawan sa’bon Allah kuma, malam inaso a taimake ni da shawara akan hakan ?

(Daga sadis Auwal).

AMSA:
-------------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan uwa, ina fatan zaka karanta wannan ‘kissar
da idon basira, domin zaka sami shawarar da kake bukata gata kamar haka:

Wata rana wani saurayi yaje wajen Ibrahim ‘dan Adhama, (‘daya daga cikin magabata), sai yace
masa zuciyata tana tunkuda ni zuwa sa’bo, kayi min wa’azi. Sai ya ce masa:“Idan ta kirawo ka zuwa sa’bawa Allah to ka saba masa, amma da sharuda guda biyar.
Sai saurayin ya ce fadi mujisu Sai yace:

1. Idan zaka sabawa Allah, to kabuya a wurin da bazai ganka ba, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, yaya za’ayi na boye masa, alhalin babu abin da yake ‘buya gareshi ???Sai yace:Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kuma yana ganinka.

2. Idan zaka sabawa Allah to karka saba masa acikin kasarsa, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina zanje, alhali duka duniya tasace ???Sai yace masa:
Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kana zaune a saman kasarsa ?

3. Idan zaka sabawa Allah to kadaina cin arzikinsa.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah, ta yaya zan rayu alhali duka ni’imomi daga gareshi suke ?Sai yace masa:
Yanzu ba kajin kunya ka sa’ba masa alhali yana ciyar da kai kuma Yana shayar dakai, Yana baka
karfi.

4. Idan ka sabawa Allah, to idan mala’iku sukazo tafiya dakai Wuta, kace bazaka tafi ba Aljanna za ka.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah ai sunfi ‘karfina, korani
zasuyi.

5. Idan ka karanta zunubanka a takardarka ranar
alkiyama kace ba kaine ka aikata suba.
Sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina mala’iku masu kiyayewa, sai yafashe da kuka yatafi yana maimaita
wannan Kalmar ta karshe.IN HAR KANA TUNA ‘DAYA DAGA CIKIN WADANNAN IDAN ZAKA AIKATA ZUNUBI, TO TABBAS ZAKAJI KUNYAR ALLAH.Tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki.
Ya Allah ka tsarkake mana zukatanmu daga sabo.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

tambaya

tamabyoyi.jpg

Shin malam ko ya halatta mace mai ciki ta daina sallah ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum
Dafatan malam yawuni lafiya.Malam don allah inaso akara mana haske akan
mene hukuncin matar datake zargin mijinta ?
Sannan malam shin ya halasta mace mai juna biyu ta daina sallah ?
Nagode.

(Daga Fateemah Muhammad).

AMSA
---------------------------------------


ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Shi Musulunci addini ne wanda ya gina al'ummarsa abisa kyautata mu'amala da yarda da juna da amincewa da kare mutuncin juna.Don hakane ma Musulunci baya yarda da duk
abinda ya zamto zargi ne, wato babu Qwararan shaidu wadanda suka tabbatar da faruwa ko
kasantuwar abin.Abinda kike zargin mijinki dashi, duk dadai ke zuciyarkita yardar miki cewar yana aikata wannan abin, to amma bakki da Qwakwarar Shaidar da zata tabbatar da zarginda kike yi masa.Yazama wajibi kicire zargi a zamanku na auratayya.

2. AMSAR TAMBAYA TA BIYU.Ba'a daukewa mai ciki sallah yazama wajibi ta kawota.Akwai aiyuka da dama na addini da ake daukewa
dan adam idan larura irin wannan tafaru akansa,amma ita sallah koda kana kwance baka iya tashi
muddin kasan a inda kake saika kawota koda jingina a bango ne.Balantana mace mai ciki wacce har takanyi wanke-wanke shara etc.Saboda haka 'yan uwa mudaina sakaci da sallah.
ALLAH SHINE MASANI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

adduoin sabbin ma,aurata

tambaya-da-amsa.jpg

Addu'o'i domin sababbin ma'aurata.

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA


Assalamu alaikum.
Dan Allah malam wacce addu'ar mutum zai karanta idan yayi sabon aure ?Kuma wacce addu'ar zai karanta idan zai sadu da matarsa ?

(Daga Mukhtar Isyaku B Musawa).

AMSA
--------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .


DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Idan mutum yayi sabon Aure anaso yadora hannunsa, akan goshin amaryarsa ya karanta
wannan addu'a kamar haka:''ALLAHUMMA INNY AS'ALUKA MIN KHAIRIHA WA KHAIRI MA JABALTAHA ALAYYA.WA A'UZU BIKA MIN SHARRIHA WA SHARRI MA JABALTAHA ALAYYA.

««FASSARA»»
Ya Allah ina roqonka Alkhairinta, da Alkhairin abin
daka dabi'antar da ita akansa.Sannan ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin abin daka dabi'antar dashi akanta.Addu'ar Saduwa da iyali kuma itace kamar haka:''BISMILLAHI, ALLAHUMMA JANNIB'NASH
SHAIDANA WA JANNIBISH-SHAIDANA MA
RAZAQTANA.
««FASSARA»»
Da sunan Allah, Ya Allah ka nisantar da shaytan daga garemu, sannan ka nisantar da shaidan daga abin daka azurtamu dashi.
Za'a karanta wannan addu'arne kafin afara
saduwar.ALLAH SHINE MASANI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like: HANYAN TSIRA

Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM,WHATSAPP, da
sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.Manzon Allah (saww) yace:"WALLAHI IDAN
ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA DALILINKA,YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAKUMMA"
Share:

mallam koh zan iya sallah da wandon

tamabyoyi.jpg

Malam ko zan iyayin sallah da wandon ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum.
Malam Tambayata itace mutum ne yake da wando guda biyu a jikinsa da dan karami da kuma babba to sai mazi ko maniyyi ya zuba shin zai iya sallah dana wajen ??

(Daga Jamilu A Aliyu).
AMSA
-----

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Eh idan maniyine zai iya sallah dashi babu laifi.Saboda hadisin da nana Aisha (R.A) take cewa:Na kasance ina sanya farcena na kankare
bushashshen maniyyi a jikin tufan Annabi (s.a.w).Kaga da najasane Annabi bazai barshi yabushe
ajikin kayansa ba. Amma idan maziyyine yanada kyau a yayyafa ruwa kafin ayi sallah da tufafin.ALLAH SHINE MASANI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969



Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM,WHATSAPP, da
sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.Manzon Allah (saww) yace:"WALLAHI IDAN
ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA DALILINKA,YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAKUMMA"
Share:

KOZAN IYA QARA GASHI, SABODA MIJINA ???

tamabyoyi.jpgKOZAN IYA QARA GASHI, SABODA MIJINA ???

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

KOZAN IYA QARA GASHI, SABODA MIJINA ???
Malam nayi rashin lafiya kaina ya kwakuye, mijina
yana bakin ciki, idan yaga kaina.Kozan iya kara gashi, don zaman auranmu ya kara
dadi ??

AMSA.

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
==================
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To 'yar uwa wata mace taje wajen Annabi (s.a.w)
tabashi labari cewa:
'Yarta tayi rashin lafiya gashin kanta yazube, kuma gashi mijinta ya umarceta data kara mata gashi,shin zata iya Qarawa ???.

Sai Annabi (s.a.w) yace mata:A'a, saboda an la'anci masu Qara gashi"Bukhari ne ya rawaito a hadisi mai lamba ta:4831.
Hadisin yana nuna cewa:Baya halatta mace taqara gashi, koda kuwa mijinta
ne ya umarceta.Saboda hakan zaisa tashiga tsinuwar Allah.
Allah shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like: HANYAN TSIRA

Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM,WHATSAPP, da
sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.Manzon Allah (saww) yace:"WALLAHI IDAN
ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA DALILINKA,YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAKUMMA"

وعليكم السلام ورحمة الله وبركاته
Share:

Shin malam ya halatta ayiwa kabari sumunti ?

Shin malam ya halatta ayiwa kabari sumunti ?
tamabyoyi.jpg

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu alaikum
Malam wai ya halatta asawa kabari sumunti ?

Daga Salihu Kankia.
AMSA:-

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
-----
DASUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
A’a kasa mai danko kadai ake iya kwa6awa a
sanya, domin kada kasa ta rufeshi.Amma sanya sumunti makarufine.sannan kuma, sanya itatuwa, yafi a sanya tukwane.
Saboda sanya tukwane zai hana wata rana a sanya wani a wurin saboda za ayi ta ganin kushewar kabarin, nasa na farko.
Domin tukunya bata lalacewa da wuri, sai tayi samada shekaru dari.Amma itace nada saurin rubewa, ya lalace (ya6ace
fiye da sauri) akan tukunya.WALLAHU A'ALAM. R's

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Advertise Your Product

Be With Me Technology

Guide Tricks Blog

Tallata Kayanka


Popular Posts

Author

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Translate