
Kallon Blue film ga ma'aurata DAGA ZAUREN HANYAN***TSIRA Slm Malam dan.ALLAH yahalatta mutumin da yake da aure yaringa kallon BLUE FILM shida matarsa ? AMSA ========================== ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ . A'a bai halattaba, yin hakan haramunne, Allah (s.w.t) ya tsinewa mai kallon tsiraici da wanda yake nunuwa. Akwai zunubi mai tarin girma, domin gudun kada mutum yafada zina yasa yayi aure, idan akace mutum yayi aure baya samun biyan bukata da matarsa ta sunnah dole saiya kalli kafirai maqiya Allah da Manzonsa suna tafka masha'a suna aikata zuna a fili yazama auren nasa bai katangeshi daga zina ba kenan. Duk ma'auratan da suka sabarwa kansu da irin wannan muguwar dabi'ar tunda wuri sudaina. Bazasu ta6a samun biyan bukata ta wannan hanyar ba. ABIN DAYA KAMATA SUYI SHINE: ================= matsayinsu na ma'aurata su cire kunya su zauna su tattauna tsakaninsu, akan shi mai gidan ko ita uwar gidan wanne abu yafiso ko wanne abu tafiso tayi masa ko yayi mata a lokacin kwanciyarsu ta aure ??? Wannan shine matakin daza su dauka amma maganar kallon B.f haramunne Allah (s.w.t) yana fushi da ma'auratan da basa kishin junansu. Da fatan ma'aurata zasu kiyaye. Allah ka aurar da matasanmu maza da mata su huta da wannan bala'in albarkacin Muhammadu Rasulullah (s.a.w). Dan Allah kudinga yin share dinsa ta facebook da kuma whatsapp domin 'yan uwanku su amfana. www.hanyantsira.blogspot.com whatsapp 09039016969 Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/ وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته