Barka da zuwa shashin musulunci manufar bude wannan shafin shine Bayyana Yadda Musulunci Ya Haskaka Rayuwarmu

ZUCIYATA

tamabyoyi.jpg

Malam zuciyata tanason aikata sa6o, yaya zanyi
na hanata ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Salam, malam a cikin zuciya ta ina jin tsoron Allah,kuma ina son bin umarnin Allah, saidai ina yawan sa’bon Allah kuma, malam inaso a taimake ni da shawara akan hakan ?

(Daga sadis Auwal).

AMSA:
-------------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan uwa, ina fatan zaka karanta wannan ‘kissar
da idon basira, domin zaka sami shawarar da kake bukata gata kamar haka:

Wata rana wani saurayi yaje wajen Ibrahim ‘dan Adhama, (‘daya daga cikin magabata), sai yace
masa zuciyata tana tunkuda ni zuwa sa’bo, kayi min wa’azi. Sai ya ce masa:“Idan ta kirawo ka zuwa sa’bawa Allah to ka saba masa, amma da sharuda guda biyar.
Sai saurayin ya ce fadi mujisu Sai yace:

1. Idan zaka sabawa Allah, to kabuya a wurin da bazai ganka ba, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, yaya za’ayi na boye masa, alhalin babu abin da yake ‘buya gareshi ???Sai yace:Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kuma yana ganinka.

2. Idan zaka sabawa Allah to karka saba masa acikin kasarsa, sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina zanje, alhali duka duniya tasace ???Sai yace masa:
Yanzu bakajin kunya kasa’ba masa alhali kana zaune a saman kasarsa ?

3. Idan zaka sabawa Allah to kadaina cin arzikinsa.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah, ta yaya zan rayu alhali duka ni’imomi daga gareshi suke ?Sai yace masa:
Yanzu ba kajin kunya ka sa’ba masa alhali yana ciyar da kai kuma Yana shayar dakai, Yana baka
karfi.

4. Idan ka sabawa Allah, to idan mala’iku sukazo tafiya dakai Wuta, kace bazaka tafi ba Aljanna za ka.Sai saurayin yace:Tsarki ya tabbata ga Allah ai sunfi ‘karfina, korani
zasuyi.

5. Idan ka karanta zunubanka a takardarka ranar
alkiyama kace ba kaine ka aikata suba.
Sai saurayin yace:
Tsarki ya tabbata ga Allah, ina mala’iku masu kiyayewa, sai yafashe da kuka yatafi yana maimaita
wannan Kalmar ta karshe.IN HAR KANA TUNA ‘DAYA DAGA CIKIN WADANNAN IDAN ZAKA AIKATA ZUNUBI, TO TABBAS ZAKAJI KUNYAR ALLAH.Tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki.
Ya Allah ka tsarkake mana zukatanmu daga sabo.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

LIMAMIN MU YA MANTA AYA A SALLAH

tambaya-da-amsa.jpg

LIMAMINMU YA MANTA AYA DAYA A FATIHA ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

LIMAMINMU YA MANTA AYA DAYA A FATIHA ?

Assalamu alaikum, malam barka da qoqari.Mal. Ya matsayin sallar da liman ya tsallake aya
guda a cikin fatiha ???
Jazakallah.
(Daga Halliru abdullahi)

AMSA.

=======================

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To dan'uwa Annabi (s.a.w) yana cewa:"Babu sallah ga wanda bai karanta fatiha ba"kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta:723.Malamai sunyi sabani akan Idan liman ya manta
aya daya a Fatiha, a sallar da take ta farilla, bai tuna ba, sai bayan yayi sallama, wasu malamai sukace zaiyi sujjadar rafkannuwa.
Amma zance mafi inganci shine:Idan har ba'a samu lokaci mai tsawo ba, to sai yatashi yasake raka'a daya.Idan kuwa an samu tazara mai tsawo tsakanin
lokacin daya tuna da kuma lokacin sallamarsa, to
zai sake sallar ne gaba dayanta, saboda fatiha
rukuni ce ta sallah bata tsayawa sai da ita, kamar yadda hadisin daya gabata yake nuni.Domin neman Qarin bayani sai aduba Fatawaa
Alajna Adda'ima:5/331.
Allah shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

MUTANE UKU ALLAH BA ZAI MUSU RAHAMA BA

tunatarwa.jpg

Mutane 3 Allah bazai yi musu rahmaba.

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

MUTANE UKU ALLAH YA HARAMTA MUSU SHIGA ALJANNAH
Manzon Allah (SAW) Yace:"Mutane uku Allah ya haramta musu shiga Aljannah.

1. Wanda ya dawwama yana shan giya.

2. Da mai wulakanta iyayensa.

3. Da wanda yake barin Iyalansa suna aikata Fasadi.

[Nasa'I, Hakim, Bazzar, Ahmad].

Ya Allah ka tsaratar damu daga fushinka.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

MANYA MANYAN AIYUKAN ZUNUBAI

tamabyoyi.jpg

Manya Manyan Aiyyukan Zunubi

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

WADANNE AYYUKANE SUKAFI KOWANNE AIKI GIRMAN ZUNUBI ?

Abdullahi dan Mas'ud yace:Wata rana na tambayi Manzon Allah (S.A.W) nace:Ya Manzon Allah a Duk cikin laifukan da ake yiwa Allah wane laifi ne yafi kowane laifi girman Zunubi a wajan Allah (s.w.t) ?Sai Manzon Allah (S.A.W) yace:

1. Ka sanya wa Allah kishiya (Shirka) Alhalin Shi ya halicce ka shi kadai. Sai Abdullahi dan Mas'ud yace tabbas wannan
babban al'amari ne.
Sai kuma me?

2. Manzon Allah (S.A.W) yace:Ka kashe danka don kar yaci abinci tare dakai a
rayuwa, dan kar kadauki da wainiyarsa.
Sai Abdullahi yace:
Sai kuma me?

3. Manzon Allah (S.A.W) yace:Kayi Zina da matar makwafcin ka.Yan Uwa kunji a duk cikin laifukan da yafi girman zunubi a wajen Allah bayan shirka.Bayan ita sai Kisan kai, ba wani laifi da ya kai lafin
Zina a musulunci girman zunubi.
Duk wanda ya dauki zina amatsayin sana'a, ko a matsayin aikin yi toh Wallahi ya gaiyato fushin Allah akan sa, kuma yana sone ya jefa Al'umma acikin masifa cikin bala'i, kuma zai gamu da
masifu, zai gamu da bala'i zai gamu da walakanci tun a duniya kuma zaiyi mum munan karshe, a
lahira kuma zai gamu da azaba mafi muni.
Allah ya kare mu daga aikata wadan nan manyan laifuka, ya kuma karemu daga sharrin shaidan,Allah ya shiryemu baki daya.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

gurare da aka haramta wa maxe ta kalla a jikin yar uwanta mace

tambaya-da-amsa.jpg

Wadanne gurarene aka Haramta mace takalla ajikin 'yar uwarta mce ?

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

Malam menene hukuncin mace tabayar da jikinta
ga mata yan’uwanta don ayi mata wanka saboda kwalliya ko irin dilka da halawa din nan wai haramunne Koda ta rufe mamanta da mazaunanta ?Idan haramun ne kenan daga ina zuwa inane
tsiraicin mace da bai kamata yar’uwarta mace ta gani ba ?
Jazakallahu khairaljazaaa.
(Daga Murjanat Sunusi).

AMSA
-------------------------------------------

ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.To ‘yar uwa malamai sunyi sabani gameda tsaraicin mace ga ‘yar’uwarta musulma.

Akwai wadanda suka tafi akan cewa:

1- Bai halatta ‘yar uwarta mace taga wani abu a jikinta ba, sai abin daya saba bayyana a tsakanin
mata.Idan suna zaune isu-isu, kamar kafa da hannu da fuska da wuya da makamacin haka.

2. Saidai abin da mafi yawan malaman fiqhu suka tafi akai shine:
Al’aurar mace ga ‘yar uwarta musulma tana farawa ne daga cibiya zuwa guiwa, kamar yadda al’aurar maza take a tsakaninsu.
Don haka bai hallata tabari wata mace takalli samada wannan wurin da aka iyakance ba.

3. Amma idan kafira ce matar to malamai sunyi bayani cewa bazata kalli wani abuba, sai abin da
yasaba bayyana, don haka sai a kula lokacin da za’aje dilka wajan wacce ba musulma ba, don kada garin neman gira a rasa ido .
Sannan a bisa wannan bayanin da kikayi, dilkar da kika siffanta zata zama bata halatta ba, tunda za’a
ga abin da shari’a bata hallatata a gani ba.
WALLAHU A'ALAM

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

shaawar boye...

tunatarwa.jpg

Sha'awar 6oye

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Wata rana Wani Sahabin Manzon ALLAH (S.A.W)
Mai Suna Shaddad Bin Aus (R.A), Yafashe Da
Kuka.Sai Aka Tambaye Shi Dalilin Yin Kukan nasa.Sai YaCe:-
"Wani Abu Ne, Da Naji Daga Manzon ALLAH
(S.A.W) Na Tuna, Shi Yasani Kuka.NaJi Manzon ALLAH (S.A.W) Yana Cewa:
Ina Jiwa Al'ummata Tsoron SHIRKA Da Sha'awar boye)"Sai Nace:"Ya RASULULLAHI (S.A .W)! Al'ummarka Zatati
Shirka a Bayanka???
Sai YaCe:"E! Amma Bazasu Taba Bautawa Rana Ko Wata Ko
Dutse Ko Gunki Ba.
Sai Dai Zasu Riqa Yin RIYA Da Ayyukansu.

2. Sha'awar Boye Kuma, Dayansu Sai Yawayi Gari Yana Mai Azumi.Sai Wata Sha'awa Daga Sha'awoyinsa Ta Bijiro
Masa, Sai Ya Bar Azumin Nasa (ma'ana ya karya azumin).(Imam Baihaqi Ya RuwaitoShi a Cikin Shu'abul-
Iman).HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKEEL!WANNAN SHINE HALIN DA YAWANCIN MUSULMI A YAU SUKA TSINCI KANSU.YA ALLAH KA TSERATAR DAMU DAGA WANNAN
BALA'I MAICI BAL-BAL KAMAR WUTAR DAJI.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Tambaya na 1...

tamabyoyi.jpg

Tambaya ta 1


DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

Assalamu Alaikum.
Malam dan Allah a boye sunana:Nice ina tare da saurayina amman ba'a gari daya
muke ba, kusan kullun muna waya amman sai yanemi muyi sabon Allah.wato mu makin imagination muna sex da juna.
(i.e masturbation).
kuma nayi ta mishi wa'azi amman kullum abun karuwa yakeyi.
Mallam matsalar itace da farko da muka hadu a lokacin I dnt knw his character saina mishi
alkawarin bazan barshi ba, zan aure shi, kuma yanzu har ga Allah na canza ra'ayi akansa saboda halayen sa.Shin mallam idan na rabu dashi menene hunkucin alkawarin danayi ?

(Daga wata baiwar Allah).

AMSA
**************************

Allah yasaka miki da alkhairi.
kuma Allah ya Qara miki tsoron ALLAH afili da boye.Tabbas irin wadannan abubuwan da kikace saurayinki yana umurtarki dasu, suna daga cikin hanyoyin da shaidanun samari sukebi domin lalata
'ya'yan mutane.Ai kinyi masa alkawarine abisa zatonki cewar shi mutumin kirkine irin wanda kowacce mace takeso ta aura.Amma tunda halayensa sun nuna cewar shi shaydani ne, kuma mai neman lalata, wato irin
namijin da kowacce mace mai addini take QIN ta aura, to tabbas yazama WAJIBI ki Qaurace masa.
(kamar yadda Malam MAI AHALARI ya fada).
Kiqara godewa Allah tunda ya tsareki daga bin ra'ayin wannan shaydanin kuma kyawun fuska ko
dukiya ko zaqin bakinsa bai rudeki ba.
**Allah yana cewa:
"KARKU KARKATA IZUWA WADANNAN DA SUKA ZALUNCI KANSU, SAI WUTA TAQONA KU"
Malamai sukace:
DUK WATA ALAQAR DA BA'A QULLA TA DOMIN ALLAH BA, TO MUSIBACE QARSHENTA"Allah ya kiyaye.Yadda kika soshi tunda farko domin Allah, to yanzunma KI RABU DASHI DOMIN ALLAH.
zaki samu lada mai yawa awajen Allah.
domin Allah yanason masu yin soyayya ko kiyayya dominsa.
Kici gaba da addu'a. INSHA ALLAHU zaki samu wanda yafishi.
WALLAHU A'ALAM.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969

Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

Advertise Your Product

Be With Me Technology

Guide Tricks Blog

Tallata Kayanka


Popular Posts

Author

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Translate