Addu'o'i domin sababbin ma'aurata.
DAGA ZAUREN
HANYAN***TSIRA
Assalamu alaikum.
Dan Allah malam wacce addu'ar mutum zai karanta idan yayi sabon aure ?Kuma wacce addu'ar zai karanta idan zai sadu da matarsa ?
(Daga Mukhtar Isyaku B Musawa).
AMSA
--------------------------------
ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Idan mutum yayi sabon Aure anaso yadora hannunsa, akan goshin amaryarsa ya karanta
wannan addu'a kamar haka:''ALLAHUMMA INNY AS'ALUKA MIN KHAIRIHA WA KHAIRI MA JABALTAHA ALAYYA.WA A'UZU BIKA MIN SHARRIHA WA SHARRI MA JABALTAHA ALAYYA.
««FASSARA»»
Ya Allah ina roqonka Alkhairinta, da Alkhairin abin
daka dabi'antar da ita akansa.Sannan ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin abin daka dabi'antar dashi akanta.Addu'ar Saduwa da iyali kuma itace kamar haka:''BISMILLAHI, ALLAHUMMA JANNIB'NASH
SHAIDANA WA JANNIBISH-SHAIDANA MA
RAZAQTANA.
««FASSARA»»
Da sunan Allah, Ya Allah ka nisantar da shaytan daga garemu, sannan ka nisantar da shaidan daga abin daka azurtamu dashi.
Za'a karanta wannan addu'arne kafin afara
saduwar.ALLAH SHINE MASANI.
www.hanyantsira.mywapblog.com
09039016969
Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like: HANYAN TSIRA
Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM,WHATSAPP, da
sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.Manzon Allah (saww) yace:"WALLAHI IDAN
ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA DALILINKA,YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAKUMMA"
No comments:
Post a Comment