Shin malam ko ya halatta mace mai ciki ta daina sallah ?
DAGA ZAUREN
HANYAN***TSIRA
Assalamu Alaikum
Dafatan malam yawuni lafiya.Malam don allah inaso akara mana haske akan
mene hukuncin matar datake zargin mijinta ?
Sannan malam shin ya halasta mace mai juna biyu ta daina sallah ?
Nagode.
(Daga Fateemah Muhammad).
AMSA
---------------------------------------
ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.Shi Musulunci addini ne wanda ya gina al'ummarsa abisa kyautata mu'amala da yarda da juna da amincewa da kare mutuncin juna.Don hakane ma Musulunci baya yarda da duk
abinda ya zamto zargi ne, wato babu Qwararan shaidu wadanda suka tabbatar da faruwa ko
kasantuwar abin.Abinda kike zargin mijinki dashi, duk dadai ke zuciyarkita yardar miki cewar yana aikata wannan abin, to amma bakki da Qwakwarar Shaidar da zata tabbatar da zarginda kike yi masa.Yazama wajibi kicire zargi a zamanku na auratayya.
2. AMSAR TAMBAYA TA BIYU.Ba'a daukewa mai ciki sallah yazama wajibi ta kawota.Akwai aiyuka da dama na addini da ake daukewa
dan adam idan larura irin wannan tafaru akansa,amma ita sallah koda kana kwance baka iya tashi
muddin kasan a inda kake saika kawota koda jingina a bango ne.Balantana mace mai ciki wacce har takanyi wanke-wanke shara etc.Saboda haka 'yan uwa mudaina sakaci da sallah.
ALLAH SHINE MASANI.
www.hanyantsira.mywapblog.com
09039016969
Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like
https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/
وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
No comments:
Post a Comment