Barka da zuwa shashin musulunci manufar bude wannan shafin shine Bayyana Yadda Musulunci Ya Haskaka Rayuwarmu

SU WANENE AZUMI YA WAJABTA A GARESU ???

tambaya-da-amsa.jpgSU WANENE AZUMI YA WAJABTA A GARESU ???

DAGA ZAUREN

HANYAN***TSIRA

TAMBAYA ???
SU WANENE AZUMI YA WAJABTA A GARESU ???

AMSA
-----------------------------
ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .


Azumin Ramadan ya wajabta akan dukkan Musulmi baligi mai hankali kuma wanda yake da ikon yi,sannan mazaunin gida ba matafiyaba.Amma azumi baya wajaba akan wadannan mutane kamar haka:

Kafiri:
Azumi baya wajaba akansa, hakanan ramuwa bata wajaba a kansa idan ya musulunta a gaba.

Karamin Yaro wanda bai balagaba.
Amma za'a umarceshi domin ya saba kamar yadda magabata suke yiwa yayansu.

Mahaukaci:
Azumi bai wajaba a kansa ba.Dalili kuwa shine:Manzon Allah yace an dauke alkalami akan mutum
uku wanda mahaukaci da yaro na cikin mutum
ukun daya ambata, saboda haka idan mahaukaci sai yarama azumi to yaro ma kenan zai rama
azumin da yasha idan ya balaga.Hakanan mai bacci da yayi jimaI saboda haka
malaman da sukace mahaukaci yarama azumi basu da wata madogara daga Alkuani ko maganar
Manzon Allah (S.A.W.).

Wanda ya gaza yin azumi saboda tsufa zai sha azumi kuma bazai rama ba sai dai zai ciyar.

Mara lafiya wanda bazai iya azumi ba to shi zai rama bayan ya warke.Amma cutar da ake tabbatar bazata warke ba, to wannan ma zai rika ciyarwa.

Matafiyi:Azumi bai wajaba a kansa ba amma zai rama.

Mai haila ko jinin biki:Baza suyi azumi ba, amma zasu rama.
Allah shine mafi sani.

www.hanyantsira.mywapblog.com


whatsapp
09039016969


Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like

https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/

وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
Share:

No comments:

Post a Comment

Advertise Your Product

Be With Me Technology

Guide Tricks Blog

Tallata Kayanka


Popular Posts

Author

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Translate

Blog Archive