BAYAN YATASHI SAI YARINKA GANIN RANA ???
DAGA ZAUREN
HANYAN***TSIRA
TAMBAYA ???
MENENE HUKUNCIN WANDA YAHAU JIRGIN SAMA
DAGA KASAR SA, RANA TA KUSA FADUWA, AMMA BAYAN YATASHI SAI YARINKA GANIN RANA ???
AMSA
-------------------
ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
Bazai buda baki ba har sai rana tafadi a idanunsa.Hakama kuma idan yatashi akwai sauran rana a
kasarsa amma sai yashiga wani garin wanda yanayin kasarsu ya sabawa na kasarsa.Ma'ana su a wurinsu rana tafadi, to sai yayi buda baki tare dasu.Domin hadisi ya tabbata daga Abu Umamata Albahiliy yace:Naji manzon Allah (S.A.W) yana cewa:"Naji sauti mai tsanani a bayan wani dutse sai na Tambaya wannan wane irin ihu ne ???Sai akace kukan wadanda ake yiwa azabane a cikin wuta domin suna yin buda baki kafin rana tafadi".
Anan ma'ana tunda yana ganin rana to a wurinsa rana bata fadiba kenan.Kuma Allah (S.W.T) yana cewa:THUMMA ATIMMUS SIYAMA ILAL-LAILI"Ma'ana
Sannan kucika azumi izuwa dare"
www.hanyantsira.mywapblog.com
09039016969
Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like
https://mobile.facebook.com/Hanyan-TSIRA-704286909673846/
وسلم عليكم ورحمت الله وبركاته
No comments:
Post a Comment