DAGA ZAUREN
HANYAN***TSIRA
ﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
Haka da nakai shekaru 28, mutanen nan dai suka matsa mini sai nayi aure. Ni nasan halin da nake ciki amma suk takuramini lokacina yayi kar in
zama tuzuru, nasan bani da wata sana'a tsayayya,amma suka addaban dole na kukuta nayi aure,
nabi shawararsu, amma ko da sau daya ba wanda ya taba taimaka maini da komai. Ina ji ina gani
abin cefane da ciyar da iyali na ya gagara dole muka rabu da matar. Haka mutanen nan suka dunga zunde na suna zagi na na kasa rike mata
daya.Lokacin da ina dan shekaru 40 ne na samu wata kwangila, ta sanadiyyar wani abokina ta Naira Milliyan 10. Suna na ya baje gari cewa na samu babbar kwangila mai tsoka. Nan da nan abokai da dangi, wadan nan mutanen dai da suke bani shawara suka yo kaina, kowa da irin tashi matsalar, sunz son rance da buktunsu daban-daban. Cikin mako daya (sati daya) na rabar musu da duka kudin nan da alkawarin zasu biya a cikin dan kankanin lokaci amma suka gaza cika alkawarinsu. Dole tasa kwangila ta bata kammalu ba aka tasa keyata zuwa gidan yarisuna kallo na
sai da na kwashe tsawon shekaru 6 sannan na samu sukunin fitowa. Lokacin dana fito dukkan wadannan mutane ban same su a kusa dani ba duk sun gujeni.Tabbas akwai.....04
www.hanyantsira.mywapblog.com
09039016969
Domin samun shafinmu a Facebook sekushiga nan kuyi like: HANYAN TSIRA
No comments:
Post a Comment