MANZON ALLAH KENAN SARKIN GASKIYA !
MANZON ALLAH (S.A.W) Yace:
Akwai wani zamani zai zoma al'ummata (acikinsu)
duk wanda yariqe addininsa zai zama kamar wanda
yariqe garwashin wuta.
MANZON ALLAH (S.A.W) yace:
Nan gaba kad'an al'ummomi zasu zagayeku (ku
musulmai) kamar yadda jama'a ke zagaye kwanon
abinci.
Sai sahabbai suka tambayi manzo cewd:
Shin bamuda yawane a lokacin ?
Sai yace kunada yawa amma yawanku taron
tsintsiyane babu shara kuma nan gaba kad'an Allah
(s.w.t) zai cire kwarjinin da kuke dashi acikin
zukatan abokan ga'barku (kafirai) kuma yasanya
muku rauni.
Sai yace son duniya da qin mutuwa.
MANZON ALLAH (S.A.W) yace:
Wasu shekaru masu yaudara zasuzo wayanda
acikinsu zakaga ana qaryata mai gaskiya kuma ana
gasgata mai karya.
Mai ha'inci zaiyi zamansa cikin kwanciyar hankali,
amma za'a riga cutar mutumin kirki.
'Yan uwa yanzu a wane irin yanayi muke ciki ???
ALLAH YASA MUGAMA DA DUNIYA LAFIYA.
Home »
ALAMOMIN ALQIYAMA.
» Halin da duniyar Musulunci take ciki a yanzu.
No comments:
Post a Comment